shiga kara, kallan wayar tai sannan ta katseta ta kalleshi, yace "shine?"
Tace "eh."
Yace "bakya tunanin ya kamata kiu hadu kafin ki tafi?"
Ta kalle tace "Ai ni Dady bansan....."
Ya katseta yace "ko me zai miki, ai sallama kika mai, muje gidan ko yayane kuyi sallama mahaifine."
Jalila tai shiru batace komai ba, a kofar gidan suka tsaya saboda sunata yima mai gadin alama amma bai ko kallesu ba.
Sai da sukai parkin ya matso yace "Daga ina?"
Hassan ya kalleshi wato har mai gadi ya canza?
Yace "kayima mai gidan magana kace Jalila nasan magana dashi."
Kamar bazaije ba sai kuma ya shiga, bai jima ba sai gashi ya dawo, ya sanar dasu cewa bai san wata Jalila ba.
Ran Jalila ya baci ta kalli Hassan idanuta suna neman tara ruwa tace "Yaya!"
Hassan ya kalli gidan sannan ya tada mota, Jalila ta kwantar da kanta a jikin window, kiran daya kara shigo mata ne yasa ta kalli wayar sannan ta kalli Hassan, ran Hassan ya baci, bai santa ba amma yasan numberta? Haushi ya kamashi ya daga wayar rai a bace, kafin Dady yace wani abu Hassan yace "baka santa ba taya kasan number ta? Inhar baka santa ba bai kamata kasan numberta ba."
Kan Dady ya fahimci abinda yake nufi har Hassan ya kashe wayar, ya kasheta ma gaba daya cikin bacin rai.
Haka suka shiga gida, Su Ummy dukansu na zaune a falo suka shigo.
Jalila na shiga ta gaishesu da gida, Abba yace "Jalila an gaji ko?"
Tak dariya tare da maida kai kasa, yace "ya zakiyi, wannan mijin naki ya zafaffa sai kin bar kasar da wuri? Kamar wanda ake korarsa."
Hassan ya kalli Abba yace "Abba kaifa ka karfafamin gwiwa akan na tafi da wuri."
Ummy ta kalli Abba da sauri tace "dama kaine?"
Da sauri yace "ni a ina? Gani fa nai hakan yakeso sai nadan sa baki kadan dan kadan fa nabi bayan hakan."
Hassan yace "kadan? Abba kaifa ka......."
Abba ya harareshi tare damai alamar yai shiru.
Hassan yana dariya yace "Ummy na!"
Sageer yace "Ummy karki wani yarda da dadin bakin yaya, matarsa kawai ya sani."
Kunya ta kama Jalila tai kasa dakai, Amira tace "kaima Yaya Sageer ya kamata ka motsa, kaga in Aunty Jalila ta tafi gidan zaiyi shiru gwara ka kawo wata."
Sageer yai dariya tare da kallan Hassan, Hassan yace "me? Badai haryanzu baka fadama ko Abba ba?"
Sageer ya sinar dakai yana dariya, Abba yace "Sageer ni aka munafirta?"
Sageer da sauri yace "wallahi ba haka bane Abba inataso muyi maganar, kasan yanzu aikin ha karu shiyasa."
Haka akai ta tsokana Ummy na hira tana kuma kukulla abubuwan data shiryama Jalila wanda zata tagi dashi.
*********
Dady kam gaba daya yau ta karemai dan kudin daya biya na hotel din ya kare kuma bashida wani, shiyasa yake ta neman Jalila akan ta taimaka mai, cikin lota ya fito ya shiga yana ta nemanta jin ma wayar a kashe daga baya yasa ya cilar da wayar tasa cikin takaici.
Kwanciya yai a cikin motar sannan ya dauko wayarsa yana duba sunaye ko akwai wanda zai iya kira, sai dai kaf wayarsa ba wasu mutane, daga su Mumy sai 'ya'yanta sai Jalila, sai number Inna sai kuma harkokinsu na business.
Bakinsa ya ciza cikin bakin ciki yace "duk kun lalatamin rayuwa, na dage ina muku bauta amma karshe ku hanani abinda na dace dashi? Gyara kwanciyarsa yai tare da kallan cikin motar, wai shine ke kwana a mota? Lalai dole ya nemo mafita, zaije ya samu Jalila gobe har kasa zai tsugunna ya nemi yafiyar Hassan da Mahaifinsa, ya tabbatar intaga halin da yake ciki zata tausaya masa.
**********
Hannu yasa ya jawota yace "me kuma kikeyi?"
Tace "bakomai, so nake kawai na karasa hada kayan nan."
Yace "Yanzu ina toilet wani abu ya fadomin, anya Dadynki bai saida gidan nan ba?"
Tace "ah haba? Ya saidashi ya koma ina? Sannan gidanda ba nashi ba? Taya zai saida musu abinda ba nashi ba?"
Hassan ya ajiyaf zuciya yace "kuma haka ne."
Tace "Bansan dai mai ke damunsa ba, na kasa gane dalilin kiran nawa."
Hassan yai shiru shima yana tunani.
Bayan sun kwanta wajen karfe shadaya hankalinsa ya kasa kwanciya, mikewa yai ya dau wayar Jalila ya fito falo.
Kunnata yai sannan ya kira wayar Dady, Ringing uku ya dauka da sauri yace "Jalila?"
Hassan cikin mamaki yace "dazu da mukazo gidanka me yasa ka kore mu?"
Jin murtar Hassan yasa yadan yi dum....
Sai dai jin kalamansa yasa yace "gidana???"
#OneLove💕🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
_Gareku duk mai kaunar littafin nan, ina tsananin godiya akan yanda kuka nuna kaunarku ga littafin nam, nagode kwarai da gaske🥰🥰OneLuv💕_
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
*79*
Dady yai shiru har saida Hassan yace "dazu."
Dady ya hadiye wani abu na bakin ciki yama kasa magana.
Hassan yace "kana ina?" Dan ya fahimci da matsala.
Dady yace "inzo ne?"
Hassan yace "eh in zaka iya, sai na sameka a waje."
Da sauri dady yace "to."
Mamaki ya kama Hassan ya bi wayar da kallo kafin yakoma ya zauna yai shiru yana tunanin rashin adalcin da akama Jal