i bacci mai dadi yai gaba dashi.
Washegari yana tashi kawai ya fita yaci abinci ya siyo kayan makulashe ya dawo ya kwanta saboda yana san gobe yaje ya ciro kudin nan yasa a account dinsa.
Ba abinda yakeyi sai dai yaci yasha ya kwanta kawai ya kunna waka yana ji.
Rayuwa ta masa dadi.
****
Yau da safe yana sallar asuba ya kasa komawa bacci saboda zumudin zuwa bank, wanka yai kawai yasa kaya ya zauna akan kujera yana kirgen lokaci, ganin lokacin baya sauri ma yasa ya fito daga hotel din ya shiga mota yaje gaban banki ya tsaya.
Karfe takwas nayi yana ganin anfara hidima yai wuf ya shige ciki.
Sama yahau sannan yaje inda ya kamata ya mika check dinsa tare da sa hannu a aljihu irin babban alhajin nan.
Kallan check din yai ya dinga juyashi kafin ya kalleshi yai kafin yace "Alhaj wannan check din waya baka shi?"
Yai murmushi saboda ya fahimci kudin ne ya tsorata su.
Yace "Menene na tambayar abinda bai dameka ba, yi sauri ka bani inaso nai transfer dinsu bank dina ne."
Mutumin yai shiru kafin ya fito daga inda yake yace "ina zuwa."
Bai fi minti 10 da fitaba sai gashi ya dawo shida wani, nan dayan ya kalli Dady yace "Alhaji ina ka samu wannan check din?"
Ran dady yadan baci yace "kunsan ko ni wanene kukemin wannan tambayar banzan?"
Mutumin ya kara sanyaya murya yace "ba haka bane, wannan takardar ta check ba namu bane, anyi amfani da irin namu ne anyi jabu, dan idan ka daga shi sama shida namu zakaga ba iri daya bane, sannan ko karfin takardar ma ba iri daya bane."
Dady cikin rashin fahimta yace "me kuke nufi kenan a takaici? Kunaso kucemin ba zaku bani kudi na bane ko kuma me?"
Yace "bawai zancen zamu baka ko zamu hanaka bane, zancen an cuceka an baka abu jabu mukeyi."
Cikin tashin Dady yace "an cuceni kamar ya?"
Yace "am sorry to say amma mu ba abinda zamu iya maka, sai dai ka koma gun wanda ya baka ka nemi ya baka wani ko kuma ya maka transfer."
Yana neman sake magana dayan ya dafashi alamar yai shiru dan ya kula Dady kamar ya gama hasala, Dady yai shiru kafin ya fito da sauri daga cikin bank din, da sauri ya fada mota sannan ya wuce gidan.
Gani yai anata sauke kaya da sauri ya karasa gun mutumin dake tsaye yana bada umarni, da gudu ya karasa inda yake yace "Malam dan Allah ina mai gidan nan?"
Mutumin cikin mamaki ya tureshi tare da cewa "Meye hakan?"
Dady a rikice yace "dan Allah mai gidan nan nake nema."
Yace "nine mai gidan kai waye?"
Dady hankali a tashe yace "bakai ba wanda na saidawa gidan shekaranjiya."
Mutumin ya tureshi da karfi har Dady ya fadi a kasa yace "kai dalla bansan hauka jiyan nan nasai gida million 50 yau kuma kazo kana tambayata maganar banza?"
Da karfi ya kira mai gadinsa yace "ya fitarmai da wannan mutumin daga gidansa.
Mai gadin ya kalleshi yace "zaka fita ko na fitar dakai?"
Dady ya mike kamar wanda zai fadi ya fita, yana fita gate ya zauna a bakin gate din..........
*******
#OneLuv๐๐ฏ *JALILAH* ๐ฏ
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
*78*
Dady yai tsutsuru a waje har baisan sanda lokaci yai ta tafiya haka ba, mikewa yai jin cikinshi na wani irin karar yunwa, motarsa ya shiga ya zauna idanunsa sun firfito, tada motar yai ya wuce hotel din da yake ciki, yana shiga ya wuce cikin toilet ya sakarma kansa ruwa ruwa na zuba yana tunanin abinda ke faruwa, yanzu wannan uban zuzurutun kudin ya wuce kenan ko me? Gidansa fa?
Jiyai kansa yayi dumm da karfi ya saki wata irin kara na takaici ya daki bango da hannunsa, sam bai kula da jinin dake ta zubo mai ba, hucci kawai yakeyi kamar wani kumurci.
Haka ya fito yasa doguwar riga ya bude window yana kallan gari, gaba daya kansa ya rufe yama rasa ta ina zai fara yin tunani, ga wata uwar yunwa da yakeji, mikewa yai ya dau jakarsa ya fita reception.
Gun masu aiki a hotel din ya nufa yace "yanaso a bashi karamin daki da toilet sai a bashi ragowar kudinsa."
Nan sukacemai ai bazai yiwu ba tunda dai dama na kwana hudu ya biya kuma yanzu yayi biyu bayanda zasuyi, bakin ciki ya kara mamayeshi gashi dama ragowar na account din ya kwashe ya biya saboda yana ganin yanzu kudi sunzo masa.
Ya baza tagumi a cikin reception yaji ance "dunoyar tama zafi ne?"
Juyowa yai ya kalleta, yarinyace wacce batafi shekara 30 ba tasha gayu nagaske, Dady ya kalleta sannan ya juya yana kallan wani gun.
Kallansa tai sannan tace "kudi kake nema?"
Idanu ya kura mata baice komai ba, tace "ka biyoni zan baka."
Ta fada tare da ajige key din dakinta a kusa dashi sannan ta mike, ta dan matso kadan tace "1day 500k, deal?"
Dady da sauri ya dago ya kalleta, kashenmai ido tai sannan ta mike tai ciki.
Dady ya bita da kalli sannan ya dauki key din ya mike tare da jan jakarsa, haryakai hannunsa zai murda dakin ya tuno Jalila, Safeena, Sultan da Yasmeen.
Da sauri ya saki kofar sannan ya fara ja baya baya, yana san kudi na fitar hankali dan shi burinshi