tace โeh, a gidan Goggo zai zauna saboda exams.โ
Yace โban gane ba.โ
Nan ta fadamai yanda sukai, hannu yasa ya shafi kanta ta baya yace โahh baby na u are sooo kind....โ
Tace โkai yaya....โ
Tana tura kofar dan dakin yai shiru yana bin dakin da kallo, gaba daya jikinsa yayi sanyi.
Ganin yanda yake bin dakin da kalli yasa ta matso ta rungumeshi ta baya tare da kwantar da kanta a bayansa....
#OneLuv๐๐ฏ *JALILAH* ๐ฏ
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
*77*
Hannu yasa ya juyo da ita saitinsa sannan ya rike hannunta, janta yai zuwa katifar dakin, kwantawa yai sannan ya miko mata hannu, murmushi ta sakar masa sannan ta kwanta kusa dashi itama, jawota yai ya rungume ta ajikinsa sannan ya shafa bayanta yace "Yau na kwanta a inda Baby take kwanciya shekara da shekaru."
Jalila ta dago da fuskarta ta kalleshi tace " katifarka duk tayi kura ka kwanta."
Yace "katifar da kika sha kwanciya akai ko me tai ai banaji zan kasa kwanciya."
Jalila ta kankance ido tana kallansa, yace "wannan kallan fa? Ko kin dauka karya nake?"
Tace "ah haba wani karya kuma kawai dai ina tunanin da Yayan nan lafiyarsa kalau, yan mata nawa zaiso kafin ni? yan mata nawa ne zasu soshi kafin ni?"
Yatsa yasa ya dungure mata kai yace "wadannan tunanikan naki sai nadau mataki babba akansu."
Tai dariya zatai magana yace "badai a kasan ranki kina farin ciki da rashin lafiyar danai ba ko?"
Da sauri tace "ni? Inji wa?"
Hannunta ya riko ya matse yace "fadamin gaskiya....:"
Dariya ta dinga kyalkyalawa saboda yanda ya mata rikon tana cewa "yaya wallahi da zafi...."
Ganin yanda take dariya sosai yasashi a wani farin ciki, can yace "Jalila."
Ta kalleshi bayan ta daina dariyar, yace "Shigowata dakin nan sai na fara tunanin kamar ban kyauta miki ba, zan daukeki daga inda zakiga Goggonki saboda wasu burika nawa, nasan ci gaba da karatu da kuma san kadaicewa."
Kallansa kawai takeyi fuskarta dauke da murmushi, kara kwantar da kanta tai a jikinta tace "ka manta me nace ma tun farko?"
Yai shiru yana saurarenta, tace "ko ka manta nacema duk abinda ka tsara daidai ne a gurina?"
Ta dago ta kalleshi sannan tace "Goggo ma dinga yin waya, sannan kaima ai is not easy ka rabu da su Ummy da su Abba."
Shiru yai kafin yace "nifa kinsan me na miki?"
Tace a'a yace " course daya na cike mana fa ni dake."
Dariyarta ta kunshe tace "shiyasa a sanda Abba ke tambayata wani course nakeso kaketa shashantar da zancen?"
Hassan yai dariya yace "eh mana, nafiso mu shiga tare mu fito tare, sannan kinga in muka tashi aiki muyi a company din Abba a tare."
Jalila tace "Hmm wannan wayan yayi."
Yace "ai dama yayi sosai ma."
Jalila tai dariya kawai......
Su Mumy na gama hada kaya suka fito suka shiga motarsu, ita kuma da Hassan sukadau Sultan, Hassan yaba Mumy kudi suka fito, dady na tsaye zuru yana kallansu, Yasmeen sai kuka take ita gun Dady takeso.
Shikam Dady haushi ne ya isheshi har dakin Sultan ya shiga dan suyi magana amma Sultan yaki kulashi.
Haka ya fito rai a bace.
Mumy kam shiru tai kawai a cikin mota gaba daya ta kasa ko furta kalma daya, itakam Safeena kanta ta kwantar akan kujera kawai.
**************
Sun isa gidan Goggo, Sultan ya tsaya a jikin kofar shiga falon, Hassan ya sa hannu a kafadarsa ya jashi ciki, Goggo tana ganinsu ta mike cikin jin dadi, Jalila kam da sauri aka wuce aka fada jikin Goggo.
Goggo tasa hannu ta tureta tace "ko kunya ma bakyaji mutum inya girma ai yasan ya girma."
Ta koma gefe tare da turo baki, Goggo ta kalli Hassan tace "Yasu Ummy?"
Yace "suna lafiya."
Ta kalli Sultan wanda yai shiru a tsaye, tace "Sultan! Ba magana?"
Ya tsugunna kansa na kasa yace "Goggo ina wuni?"
Tai dariya tace "Haba Sultan menene hakan? Kamar wanda baka sanmu ba?"
Yai shiru kansa a kasa.
Sun danyi hira kadan kafin su taso su tafi......
***********
Takardar gidan ya mika musu tare da sa hannu akan takardar shaida sannan suka bashi check na kudin gidan, kallan check din dake dauke da kudi zunzurutu har million 30, gidan ya kara daraja ne saboda akwai furnitures, wani irin dadi ne ya kamashi, dan shikam gani yake ya cucesu ne, ya danne farincikinshi yace "kamar yaushe zaku dawo?"
Mutumin ya kalleshi yace "eh, muna sa ran gobe dan dama iyalaina zasu baro garin Abuja ne su dawo nan."
Dady ya jinjina kai yace "bakomai ni yau zan tashi, nagode sosai."
Sukai musabaha sannan suka fito, dady cikin murna yai daki dan dama ya gama tattara kayansa, sannan ya koma ciki, wani irin ihu naji ya saki na farin ciki sannan ya kara gyara kayansa kawai ya jawo ya lodasu a mota ya ja ya fita.
Hotel kawai ya wuce ya kama katan daki suit room, ya kwanta cikin jin dadi, ya fara tunanin menene zai fi mai? Business zai fara ko kawai ya fita yawon shakatawa? Inya dawo ragowar ya nemi gida karami.
Haka yai ta sake sake marasa ma'ana, har wan