ira da gidan cika ciki, mutuwa kuma anbarma wanda akayima)
********
Tsaki yai tare da cillar da wayar kan gado dayaga sakon Safeena akan cewa Inna ta rasu, a fili yace "Ankarama kasa nauyi."
Ya kwanta kawai tare da neman yin bacci.
Sai dai duk yanda yaso yai baccin nan ya kasa, daga ya kwanta sai ya farka a razane, mikewa yai ya dara bankan ruwa, tare da komawa kan kujera ya zauna......
#OneLuv💕🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
_Gaisuwa tare da sakon godiya gareku Mom Farhan, Haske da Meela Adeel wanna shafin naku ne 🥰🥰🥰🥰Much Luv
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
Tuba nake jiyaan jini dif kamar wutar nepa🙈
*75*
Tana shiga daki ta jingina da jikin kofa tana maida ajiyar zuciya, itakam Hassan nema yake ya maidata mara kunya.
Jin an murda kofar yasa ta kalli jikin kofar inda take a jingine, yace "wallahi ko a bude ko kuma in na shigo in wahalar da mutum."
Jalila tace "menene wahalar?"
Yace "Ayya wallahi in na irga uku ba'a budemin ba? Hmm ban masan ta ina zan fara ba."
Guntse dariyar ta tai tace "nima sai na kira Ummy."
Yace "wacce Ummyn? Ai kema kinsan Ummy tawa ce, ko kwace akesan min ne dama ban sani ba."
"Zan faea irgawa fa, kuma ko wacce number na kira tana dauke da babban bashi wanda kiss kadai bazai biyashi ba."
Daga kofar tai ta shige can cikin dakin, yana shigowa ya bita da inda tai, da sauri ta haye gado tare da saukowa daya bangaren, tana kokarin nufa kofar yai gudu ya rufe kofar sannan ya fizgota suka fadi kan carpet.
Wani irin dan kara yai tare da cewa "shikenan an karyani."
Dagowa tai da sauri gabanta na faduwa, ta lleahi idanunta sun firfito.
Cikin tsananin tsoro tace " Yaya? Ina ne? Nashiga ukuna."
Hannunsa ya langwabar yace "nan ne, nikam kamar kashin gun ma ya karye."
Gabanta ne ya kara faduwa a tsorace ta kalleshi sannan ta shiga taba hannnun, tsabar tsoro sai ma taji kamar ya karye din, tana tabawa yana cewa "wash Allah na...."
Jalila ta kar rikicewa tace "Yaya tashi muje asibiti, nashiga ukuna."
Idanunta duk sun canza, yadan karkace kai irin abin zafin nan yace "Jalila kaini na kwanta kawai ba sai naje asibiti ba."
"Yaya kargun yai tsami gobe azo kasha wahala."
Yadan kara raunane fuska yace "yanzu insu Ummy sukaji kin karya musu d'a mai zasu ce? Ki bari gobe sai mu fita ba tare da kowa ya sani ba."
Jalila tai shiru tana tunani, yace " kinsan dai in Ummy taji kin karya mata d'a akwai karamin matsala ko?"
Jalila tai shiru tana tunanin yanda Ummy ke san Hassan, yawo ta hadiya sannan ta kalleshi.
Yace "kaini na kwanta bakomai insha Allah."
Jalila idanunta sukai raurau gaba daya itakam batasan ma ya zatai ba, yace "ni nace ki kaini na kwanta ba wani abun."
Jalila ta dagashi yanata wani wash, ta kwantar dashi.
Yace "dan bani ruwa nasha."
Da sauri ta juya ta dauko mai ruwa a fridge ta matso ta bashi, yace "bazan iya mikewa ba."
Da sauri ta ajiye ruwan ta shiga kokarin dan jinginar da shi, sannan ta miko mai ruwan ya amsa da dayan hannun ya fara kokarin yanda zaiyi ya bude, da sauri ta amsa ta bude mai sannan ta mikamai, amsa yai da hagu yasha.
Yana gamawa ya mika mata jarkar ta amsa, yace "bari na kwanta dan buguwar tasamin ciwon kai, idanunta suka kara raunana tace "yaya Allah muje asibiti naba su Ummy hakuri."
Yace "karki damu Baby, Kinga Ummy tanada hakuri tana kuma da sanyi sai dai bata kyale wanda ya tabani ko kadan, kinga mubar maganarnan."
Jalila ta kalleshi sannan tace "to."
Gyaramai kwanciya tai sannan ta zauna a gefenshi, tare da rike mai dayan hannun.
Yace " banfa ci abinci ba tun na safen nan ga yanzu har an kusa magrib."
Tace "bari naje kasa na zuboma nasan tunda Ameera ta dawo tayi girki."
Ya daga kai kamar wanda baya magana, tace "sannu." Sannan ta mike ta fita, tana fita yai dariya yace "ahh baby nah." Ya jawo pillow ya rungume.
**********
Kallansa yai kafin yace "kana nufin bazaka bani kudina ba kenan ko me? Ni na kasa fahimtar inda ka dosa ne."
Wani mugun murmushi yai yace "wai kai da a haukarka kana tunani ni zan bi wadanda muka rabama kudi ince su dawo dashi ne ko me?"
Cikin zafin rai Dady yace "dama ba sun amshi kudin bane dan su bani mukami? To tunda bai samu ba basai su dawo dashi ba?"
Wata dariya yasa mai wanda ya kara kular da Dady yace "stop dreaming Abakar, dama nine na damu mu baka wannan mukamin ko saboda nima na samu abinda nake so, ko da dan haukarka da karamin tunani ka dauka 'yan board din ne suka amince a kawo ka a baka matsayin nan?"
Kallan mamaki Dady yakemai kafin yace "ba hakan bane?"
Director din yasa dariyar mugunta yace "ah haba? Abinda ka dauka kenan? Saboda na basu kudinka na lalabasu ne yasa kaga suna daga wuya akan a baka mulkin nan, kudin daka raba musu ne yasa suka bi bayanka bba wani abun ba."
Dady ya matso a zuciye ya cakumeshi yace "ni zaka wulakanta? Kasan ko ni wanene?"
Cikin karfi ya fi