hucci, kamar wani kumurci sannan ya bugawa Hassan wani banzan kallo.
Hassan kam ganin yanda yake kallansa yake muzurai yasa shi yin wata dariya tare da cewa "bani na kar zomon ba, sannan ni na taba ganin wannan karfin halin?"
Cikin tsananin fada yace "karfin hali? Karfin hali fa kace, ka san wace irin rayuwa nai har na kawo wannan ranar?" Yadanyi kara cikin karaji yace "who are u? Da har ka isa ka wargazamin abinda nake shiri shekara da shekaru?"
Baa mumy taja saboda tsoron da Dady yake bata, Hassan ya hade fuska yace "rayuwar dakai? Wani ne ya saka? Kai fa ka sa kanka, sannan kai tambayar who am i? Nine wanda har karshen rayuwata indai har inada dama bazan taba barinka ka saci abinda ba naka ba."
"Sata? Sata nai? Uban waye yacce haka ake sata?"
Yace "To sanar dani in ba sata ba menene? Tsabar san zuciya ka wulakanta iyayenka, matarka, yarka, sannan yanzu kake neman ka sace abinda dayan matar da 'ya'yanka ke da shi."
Cikin tsananin zafin rai ya matso ya sa hannu da karfi ya hankade Hassan, baya yai saura kadan ya fadi ya rike teburin dake gun.
Dady yayo kanshi cikin fada yace "uban waye ya baka damar shiga rayuwata? Uban waye?"
Yanda yake yi ne yasa Hassan ya kura mai ido yana kallan ikon Allah, gaba daya ma mutanen dake gun ma kowa kallan mamaki yake mai, Mumy kam hawaye ne kawai ke zubo mata, cikin masifa yake kallan Hassan yace "Uban waye nace? Duk duniya duk wanda ya kuskura yace zai hanani abinda nasa gaba wallahi zan iya mai abinda ni kaina ban san zan iya ba."
Mamaki ne ya kara kama Hassan yace "ya zamuyi?"
"Dame?" Dady ya fada a harzuke, Hassan yace "dan banaji zan dakata daga nan, har kasa na fara zakuwa naga mai zaka iya aikatawa."
Cikin tsananin zafin rai da bakin ciki, Dady yakai hannu ya naushi Hassan, wanda sai da ya fasa mai gefen bakinsa, ya daga hannu zai kara Sageer ya rikeshi, Dady ya juyo cikin tsananin masifa yace "menene hakan?"
Hassan ya mike ya goge bakinsa, yace "ya zamuyi yanzu kuma?"
Dady ya mai wani kallo, Hassan yace "Sageer baka tunanin ya kamata a koreshi daga aiki?"
Sageer yace "ai ba sai ka bata bakinka ba Yaya, Zakai resigning ne ka fita da martabar ka ko kuma kafisan mu koreka?"
Dady yace "mene?"
Sageer yace "ba dai kana tunanin duk wannan bugun dakai a banza kayi shi ba? Sai dai fa kayi hakuri dan duk na dau video ina jiran naji uzurinka dayasa ka naushi investors din ku."
Dady ya zaro ido ya kalli Hassan gani yai Hassan ya mai wani murmushi sannan ya matso ya danyi ajiyar zuciya yace "in zaka saida shares dinka na company in gari yama zafi ka kawo Jalila zata siya."
Hassan yai gaba ya barshi a gun, cikin takaicin hali irin nasa, Sageer yace "sai naga resignation letter gobe a sabon office dina." Ya juya ya fita.
Dady ya saki wani irin ihu wanda ya kara razana Mumy.
Sani ma juyawa yai ya fita dan shikam hankalinsa ya kasa jawomai cikaken abinda ke faruwa.
Dady ya matso kusa da Mumy ya daga hannu ya sharara mata mari, ya kara daga hannu ya sake mata wani sannan ya nunata da yatsa yace "ke har kin isa ki sa wannan dan iskan yaran yacimin mutunci?"
Kallansa tai tana hawaye tace "Dear."e
Da yatsa ya kara nunata yace "don't you dare call my name like that."
Ya matso kusa da ita sosai yace "ni kika ci amana saboda bakyasan na zama wani abun ko? Na miki saki daya."
Kawai taga ya juya ya fita, gaba daya jitai kanta na wani irin juyawa dan ta kasa tantance takamaimai meke faruwa.
Batasan yawan mintinan da ta kwashe a tsaye ba kamar mara numfashi.
Yanda wayarta ke ta zuba kara ne yasa ta farga, daga wayar tai ba tare data dubama wanda ya kira ta ba.
"Mumy ki zo gida yanzu." Muryar Sultan taji a rikice yana fadar haka.
Da sauri ta fito ta fada mota sukai gida, wasu gardawa ta gani a cikin harabar gidan, gefe kuma Sultan ne a tsaye.
Tana zuwa ta karasa gunsu tace "lafiya?"
Turo mu akai akan ku tattara kayanku ku bar gidan nan.
Cikin mamaki tace "mu bar gidan kamar ya kenan?"
Yace "ko ku bar gidan gaba daya ko kuma yace ku koma boys quaters."
Yanzu kam ta gane wanene ya turo su, waya ta daga ta kirashi.
Kamar bazai daga ba sai taji ya daga, cikin mamaki tace "Abakar me kake nufi akan munar gidan da mahaifina ya gina?"
Yace "kema kiji in aka kwacema abinda yake naka ya kakeji."
Tace "ni menene naka dana kwata?"
Tambaya kike?
Tace "badai company dinmu kakeso kace ba?"
Yace "ko ma menene magana ta kare, ke kika bani gidan nan da kanki sai kisan inda dare ya miki."
Tace "zan san inda dare yamin amma 'ya'yanka fa?"
"'Ya'ya? Ki tabbatar kin kwashesu."
Hawayenta dake zubowa ne ya karo, tace "nikam Abakar tunda nake dakai ka taba min so na tsakani da Allah kuwa?"
"So? Wasan yara kika koma yi kuma?"
Mumy ta toshe bakinta saboda kuka na neman cin karfinta, kawai kashe wayar tai ta kalli Sultan tace "wuce kaje gidan Kawu, ni zan koma asibiti."
Yace "wai mumy meke faruwa ne?"
Tace "jeka in na dawo mayi magana."