a kofar dakin, yanna zaune yana latsa waya ta shigo, kusa da kafarsa ta zauna dan yadan jasu sama.
Sa kanta tai saman gwiwoyinsa, ta dan karkato da kanta gefen da wayar take tace “Yaya! Shine ka gudu ka barni?”
Kallanta yai tare da ajiye wayar yace “Bansan me zance miki bane, shiyasa na taho.”
Ta dan rufe baki kadan kafin tace “me zaka cemin kamar me?”
Yace “mahaifinki ne, me zance?”
Kanta ta kwantar akan gwiwar tasa kafin tace “mahaifina ne sai dai tunda nake dashi Yaya ban taba zama dashi munyi maganar mutunci ba, duk maganar da zata fito daga bakinsa zakaji san zuciya ne da tsantsan san kai.”
Hassan yai shiru yana mata kallan tausayi, murmushi tai kafin tace “ sai dai Yaya duk yanda naso na gane na kasa fahimta.”
Ya mata kallan rashin fahimta, tace “wani irin uba ne Dady? Yaya duk yanda naso na kasa gane wa.”
Fuskarsa ya sa ko kusa da tata, yace “wanda baisan baiwar da Allah ya mai ba?”
Tace “baiwa?”
Kiss ya mata yace “baiwar yarinya kamarki mana.”
Idanu ta kankance tana kallansa kafin tace “ahh yaya.”
Murmushi yai kafin yace “yau kinsan mu biyu ne a gidan nan?”
Murmushi tai sannan tace “kafin mu zama mu biyu kadan taimakamin kadan.”
Name? Tayaki breakfast din zanyi? Ya fada yana dan kamo gefen cikinta.
Dariya tasa tace “kai Yaya!”
Yace “ba su bane?”
Tace “ka taimakeni kar Dady zuciyarshi tai nisan da bazata taba waiwaye ba.”
Yace “kamar ya?”
Tace “banaso mahaifina idanunsa ya rufe, ina tsoron halin da zai afka, baya tunanin komai sai kansa, shiyasa nakeso a dakatar dashi haka daga kan san kansa da yakeyi, ya fahimci yanada responsibility’s da kuma abinda yafi shikansa daraja.”
Yace “yanzu me kikeso ayi a tsayar dashi?”
Tace “dan Allah ka taimaki Mumy, hakkinsu ne company din nan, mahaifinta da mahaifiyarta sune sukasha wahala gun ginashi, taya Dady zai zo lokaci daya ya nemi kwacewa? Bayan na tabbatar da yayi hakuri Mumy yanda take sanshi da kanta ma zata bashi, kaga alama ce ta san zuciyata da tsantsar burin rayuwa ne yake damunsa, wanda ya rufemai ido daga taimakon da aka mai, yake ganin kamar komai ya cancanta ne shiyasa ake mai?”
Hassan ya sa hannunsa yaja kumatunta kamar wata baby sannan yace “ohhh wannan babyn da alama ta mike tsaye.”
Bai saki kumcin nata ba ta shiga kokarin magana tana cewa “Yaya Please!”
Dariya yai yanda tai maganar yace “to ni kinsan bansan kan harkar ba, ta ina zan taimaka miki?”
Tace “ muje mumy sai tama bayani, lokaci yana kurewa.”
Yace “Hmm umm.” Cikin shagwaba yai tasa dariya tace “da alama in an gama wannan zan kara nema amin abin nan.”
Fuska ya hade yace “haka kawai ina murna zamu zauna mu biyu yanzu kuma kinzo da wani zance daban?”
Tace “sry yaya.”
Ajiyar zuciya yai sannan yai gaba.
Da kallo ta bishi sannan tai murmushi, bin bayansa tai.
Kasa suka sauko Mumy nata amsa waya tanata magana da Sani.
Tana ganinsu ta kashe wayar tare da gyara zama.
Hassan ya sauko kofar Sageer ya nufa tare da yima knocking.
Sageer da ya bude kofar ya kalleshi.
Hassan yace mai “Sageer dan fito plx.”
Fitowa yai tare da rufe kofar.
Jalila kam na saukowa kitchen ta nufa kawai ta cigaba da harkarta.
Duk da hankalinta nakan abinda ke faruwa a falo sai dai ta sa wa ranta abu daya, duk abinda Hassan ya yanke kawai yayi, dan bazata tilastamai akan abinda bayaso ba.
Mumy ce ta kalli Hassan wanda yacemata “fado abinda kikeso ayi muji.”
Nan Mumy tamai bayani kamar yanda Sani ya mata, tace “duk yanzu kudin dake running a company din 80% kudin Mahaifinku ne, hakan yasa kuna da hujjar kwatar company din kuba wanda kukeso in har bamu biyaku kudin da kuke bin mu ba.”
Sageer yace “amma contract din ai kamar lokacin biyan nada tsayi.”
Tace “eh, sai dai nunawa zamuyi kamar abin yazo.”
Hassan yace “nuna wa zamuyi? Har a yaushe muka zama mu?”
Mumy tace “bada wani abun na fada ba, kuyi hakuri dan Allah.”
Hassan ya kalleta sannan yace “na kasa fahimtar wani abu, in an amshi company daga hannun mijinki wa kikeso a ba?”
Tace “ni kaina bawai so nake ba, saboda koda wasa ban taba burin mulkar company din nan ba, ni kaina shi nakeso aba sai dai bata wannan hanyar ba.”
Hassan ya mata wani kallo dan shikam ya dai jitane.
Yace “Sageer ya kake gani?”
Sageer yace “bari na kira Abba muyi discussing.”
Ya fada tareda mikewa.
Ganin za’a barsu su biyu yasa ya mike ya shiga kitchen.
Ta banyanta ya tsaya tana soya yankanken kayan miya akan frying pan.
Tana ganinshi ta juyo tana kallanshi.
Karasowa yai ya sa hannunsa ya zagayo da ita ta cikinta ya kwantar da kansa a kafadarta yace “kallanfa?”
Tace “ya kukai?”
Yace “kawai dai.”
Murmushi tai kafin tace “Thanks alot Yaya.”
Yace “banasan wani thanks kawai zanbi bashi ne dan sai an biyani.”