IATION*
*71*
Mumy ta kalli Hassan idanunta sun ciciko, idanunta duk sun koma kalar tausayi, ta kara daga hannunta alamar tsananin neman taimako, tama kasa magana sai hannunta kawai datake ta murzawa.
Hassan kam Jalila ya kafa ma ido yana kallanta, wacce tai tsuru tana bin Mumy da kallo.
Sageer ne ya kalleshi yanda yaga yana kallan Jalila ne yasa yace “Yaya?”
Hassan ya kalli Sageer sannan ya kalli Mumy, daurewa yai yace “meke faruwa?”
Mumy ta kara kallansa idanta duk ya canza zuwa tausayi, kallan inda Jalila take tai a hankali tace “Jalilah?”
Jalila wacce gabanta ke ta dukan uku uku tana tsoron kar ace wani ya mutu, tsoron matsowa takeyi, Mumy ta kara cewa “Jalila!”
A hankali Jalila ta fara takowa zuwa inda take, tana tafe gabanta na wani irin faduwa, kusa da Hassan ta matso ta tsaya a hankali itama tace “Mumy menene?”
Mumy ta kalleta tace “Jalila ki rokarmana mijinki da mahaifinsa su taimaka su dakatar da mahaifinki.”
Cikin rashin fahimta ta kalleta tace “dakatar dashi kamar ya?”
Nan mumy ta kwashe abinda ke faruwa ta sanar musu sannan ta dora da cewa “bawai hanashi company din nakesan yi ba, dan ni a gurina yafi kowa dacewa daya mulki company din, sai dai ina tsananin tsoron kar san zuciya ya jefashi cikin wani halin, sannan bansan me yake kitsimawa a ransa ba, ance yanata duba takarda a gida, da farko ban kawo komai a raina ba sai dai bayan na taho ina hanya na fahimci me yake nema, takardun gidan da muke ciki yake nema, dan dama tun shekara uku da suka wuce nasa aka canza sunan gidan daga sunana zuwa nashi, saboda na kwantar mai da hankali, kenan korar mu zaiyi daga gidan, ni duk na rasa me Abubakar yake kitsimawa a kwakwalwarsa.”
Hassan wanda ko kadan baiyi mamaki ba yace “yanzu halayen mijinki kike sanar mana anan? Ko kuma halin da kuke ciki ke dashi?ni na kasa fahimta.”
Mumy tace “Hassan ka dubi girman Allah ka taimaka mana, na tabbatar in wani abu ya samu company din Inna wallahi mutuwa zatai.”
Yace “Rai a hannun Allah yake, in lokacinta yayi banaji ke ko ni mun isa mu dakatar dashi.”
Ya fada tare da juyawa ya wuce sama.
Mumy ta bishi da kallo kafin ta matso kusa da Jalila, hannunta ta riko tace “Jalila?”
Jalila ta kalleta, idanunta sun ciciko itama, Mumy tace “Jalila na san bamu kyauta miki ba ko kadan, ke da mahaifiyarki, mun wulakantaku daidai wulakanci, sai dai inaso ki dubeni ta fuskar fahimta bawai dan ke akayima ba, a’a ki dubeni a matsayinki na mace, ya zakiyi idan wanda kike masifar so rana daya yazo miki da mace sannan da tsohon ciki? Ya zakiyi in mijin da kike masifarso ya nemi ku barsu su zauna a muhallinki? Ya zakiyi in kikaga mijin naki baisan darajarsu ba, basu isheshi kallo ba bare ya nuna damuwarsu akansu?”
Jalila tai shiru tana kallanta, Mumy tashare kwallarta tace “Nasani bazaki fahimceni ba, na kuma san ban kyauta muku ba daga ke har Goggonki ko da Abakar bai nuna damuwarshi akanku ba ni kuma baikamata na maidaku kamar masu aiki ba, sai dai Jalila ki dubeni a matsayin ba kowa ba, dan Allag ki ceshi mai neman bukata, Jalila Inna tana cikin wani mawuyacin hali.”
Jalila tai shiru tama rasa me zatace muryar Sageer taji yace “ Please in kin gama ki fita.”
Shima ya wuce ciki dan shikam gani yake ko kadan basu cancanci a taimaka musu ba.
Mumy ta kalli Jalila ta kamo hannunta tace “Jalila!”
Jalila ta daure tace “Mumy zan shiga ciki.” Ta karasa tana dan zare hannunta.
Jalila ta juya zata tafi,muryar mumy taji “Safeena ta dawo.”
Cikin mamaki Jalila ta juyo ta kalleta tace “ta dawo daga Abujan?”
Mumy ta girgiza kai tace “ba abuja taje ba, fita da ita abroad mukai karatu sai dai alhakinki ne inaga yasa gashi ta dawo ba karatun ba kuma jin dadin, ta fita a banza mun kashe kudi a banza sannan me makon ta dawo cikin farinciki ta dawo cikin kunci.”
Jalila tai shiru tana kallan Mumy, kafin Mumy tace “kinga yanda rayuwa take Jalila, a da bamu daukeki a komai ba, yar mu kawai muka sani yanzu gashi kece a matsayin komai, ki duba darajar da Allah ya baki, ki rokarmana Sirikinki da mijinki su taimaka mana.”
Jalila tai shiru, sai dai ya zatayi? Ko da ace naman jikinta suka dinga yanka, yan uwanta ne, duk duniya batada kamar Safeena, Sultan da Yasmeen, dan jini ba wasa bane.
Yanda Mumy ke kara rokarta ne yasa tace “bari na mai magana, sai dai ko da wasa Mumy karkisa ran zasuyi abinda kikeso, ni dai zan yi iya nawa ne, ba kuma dan kowa zanyi ba sai dan Allah da darajar yan uwantaka.”
Mumy ta hau gyada kai tana cewa “nagode Jalila, nagode.”
Jalila ta shiga kitchen ta rage gas sosai sannan ta fito tai sama, Mumy ta bita da kallo, rayuwa kenan, wai su da sunyi tunanin cutar da ita sukai, sun killace tasu, sai gashi ashe daukakata sukai, hawaye ne ya kara taruwar mata sai yanzu hankalinta kadan kadan yake kai mata manufar Abakar, yanzu kam ta fara tantama ma in har yana santa.
Jalila ce ta tur