Tace yana fitowa waje yai, sai naga Sagir ya bishi.
Ya karayina Ahmad godiya sannan suka fita.
Hassan na zaune a can gefen asibitin ya kurama kasa ido yana karzar hannunsa na dama da farcen babban yatsarsa na hago, Sadiq na gefensa kadan a tsaye.
"Inama Allah ya d'auki ransa a wannan lokacin? Babban bakin cikinsa bai wuce yanda iyayensa ke fama a kansa ba, gaba d'aya bayasan ya zama haka, sai dai ya zaiyi?"
Sagir ne ya matso da sauri ya sa hannunsa ya tare hannun damarsa yace "Yaya!"
Kallansa yai sannan ya kalli hannunsa wanda sam bai kula ba ashe ya karje hannunsa har ya fara jini.
Hannun Sagir ya matsar sannan yace "I'm okay."
Sagir cikin tausayawa yace "muje mota gasu Ummy sun fito.
Mikewa yai suka shiga mota.
Duk yanda Abba yai akan yai bacci ya kasa, Aina? Kai ya girgiza da sauri dan yasan halin Aunty Nana, duk da yaya take agun Mumy ya tabbatar bazata yarda a aura mata Hassan ba, balle dama ta taba cewa Ummy ya kamata akai Hassan psychiatrist.
Ummy ce tace " abinda Dr Ahmad ya fadama ne yake damunka?"
Yace "ba abinda yacemin, baccin ne dai na kasa yi."
Bata sake cewa komai ba dan ta riga taji komai, Hassan da Sagir na fita ta je jikin kofar dan dama ta damu tasan cikaken halin da d'anta yake ciki, sai dai koda yaushe Abba bai fada mata.
Ba shakka itakam gobe zatama Aunty Nana magana akan Aina taji.
#OneLuv๐
[08/10, 19:19] โช+234 816 365 0557โฌ: ๐ฏ *JALILAH* ๐ฏ
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *AyusherMohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_๐ก)
*NO 8*
Dayake yau asabar ne takan dan samu ta koma bacci bayan sallar asuba saboda su kansu 'yan cikin gidan sai karfe 11 suke karyawa.
Tana idar da sallah tai addu'ointa ta baje akan katifa, Goggo ta kalleta tace "daga sallah sai kwanciya? Kya bari ai gari yadanyi haske ko?"
Jalila ta kara gyara kwanciyarta tace "Goggo bakiji baccin da nakeji ba wlh, nifa gani nake kamar ma baccin awa d'aya nai gaba daya."
"To wai jiya me kika tsaya kikai tayi ne har sai 11 na dare kika dawo?"
Jalila tadan tab'e baki tace "oho musu wai ko bako zasuyi ne ko me? Ni dai sunce inyi kwallima a babban falo sannan aka sani juya kujerun."
Ta mike da sauri ta zauna kamar wacce wata sabuwar gulmar tazo mata, tace "Goggo kinsan wai Inna ce da kanta take tsaye a kaina tana sani yanda zanyi?"
Goggo tace "to menene abin mamaki a ciki?"
Jalila tace "inna fa nace ba Mumy ba, Goggo bakiyi mamaki ba?"
Goggo tace "ni banga wani abu a ciki ba."
Jalila ta maida kanta ta kwanta tace "lalai nikam jiya da mamakin abin nan na kwana, na tabbatar bakon da zasuyi mai mahimmanci ne."
Goggo tace "ina miki magana ki tashi kiyi addu'oi amma ke gulma kike sonyi."
Idanunta ta rufe wai ita a dole bacci takeyi, Goggo tace "yi baccin karya da kyau."
Jalila tana jinta batai magana ba.
Batafi minti talatin da kwanciya ba sukaji ana buga musu kofa.
Goggo ta mike da kyar saboda ciwon kafa sannan ta kashe fitilar tasu sannan tabude kofar.
Dady ta gani a tsaye tace "Ina kwana?"
Yace " Ina Jalila?"
Tace "bacci take d'anyi."
"Bacci? Batada hankali ne?"
Goggo tace "lafiya?"
D'akin ya shiga yace "KE JALILA!"
Juyi tayi dan itakam bacci take mai dadi, Dady ya kalli Goggo yace "tasheta mana."
Goggo tace "yanzu ta kwanta."
Yace "To menene damuwata a ciki?"
Goggo ta matso jiki a sanyaye tasa hannu tadan daki kafarta kadan.
Jalila ta dan bude ido dakyar tace "Goggo dan Allah kibarni nai bacci kona awa daya ne."
Muryar Dady taji yace "kin tashi ko sai na dakeki?"
Idanunta ta bude da sauri, tace "Da Da Dy......"
Yace "will you get up"
Jalila ta mike zaune a tsorace, tace "banyi komai na Dady."
Tsananin tausayinta ya kama Goggo ace in kaga Mahaifinka tsoro kake ko kayi laifi?
Yace "tashi muje, Inna nemanki take."
Jalila ta mike tare da d'aukan d'ankwalinta ta sa a kanta.
Yana gaba tana binsa a baya har sukaje ba maganar data hadasu.
Tana shiga taga Inna a falo, tsugunnawa tai ta gaisheta.
Dady ya wuce daki dan bacci yakeji, Inna ta kalleta tace "na d'auka tunda jiya kinsan bako zanyi zaki zo da wuri dan tambayar abinda ya kamata, me yasa ne a koda yaushe bazaki dinga amfani da kwakwalwarki ba?"
Jalila tace " Yahkuri Inna."
Tace "taso."
Jalila ta mike sukai kitchen, kayan girki ta gani kala kala an fito dashi, Inna tace " inada bakon dazanyi wajen karfe 12 na safe, bayan kin gama yin abincin breakfast na gida sai ki shiga yin hidimar bakona."
Jalila ta kalli tulin kayan girkin tace "Inna me da me za'ai?"
Inna ta mata alama data matso, Jalila ta matsa kusa da ita, inna ta ce wannan vegetables din rabasu gida biyu zakiyi, d'aya kiyi miyar vegetables da farar shinkafa, wannan naman kazan pepper chicken zakiyi dashi.
Wannan d'ayar naman kazan sai ki raba biyu d'aya sai ki fere dankali ki hada kiyi chicken pie, d'aya kuma sai ki saka a cikin miyar vegetables din.
Ta kalli fruit din da ke gun tace " wannan kuma kiyi pinea