u.
Bazan miki alkawarin rashin canzawa ba ko wani abu makamancin haka, i am a human being wanda baisan ke zai faru dashi anjima ba bare gobe, amma i will try my best to love and protect you."
Kallansa kawai takeyi batasan kwalla ta tarun mata a ido ba, sai jitai ta gangaro mata, kai ta jinjina tana sharewa tace "nagode yaya, insha Allah bazan sake ba, sannan nima zanyi kokarin cire duk wata kunya dake damuna, sannan nima i will try my best to love and protect you."
Murmushi yai sannan ya miko mata hannu, itama mikomai nata hannun tai ya jawota kusa dashi, yasa kansa akan kafadarta yace "Baby yunwa, yunwa nakeji."
Murmushi tai cikin kunya tace "yanzu zakaci abinci."
Zuba musu tai a plate, chips ne da soyayyan kwan sai farfesun kaza.
Fork ta mikamai, kai ya girgiza mata alamar a'a tace "kace yunwa kakeji?"
Yace "sosai ma." Ya karasa yana rike ciki.
Tace "to naga kaki amsa kuma?"
Yace "hannuna ciwo." Tace "hannu? Garin ya ya?" Yanda tai maganar a rikice ta kara matsowa tana duba hannunsa ne yasashi yin wani lalausan murmushi.
Ahhhhhhh abinda taji ya fada kenan, kallansa tai rike da hannunsa tace "Ahhhhh?"
Ya daga kai yana kara bude baki, wato shine ya sa hakalinta ya tashi? Tace "ok, ta sa fork ta debo tace Ahhh
Bude bakin yai tare da rufe ido, jin shiru ne yasa ya bude idansa ya kalleta.
Gani yai tana cin abincinta tana kallansa tana danne dariyarta.
Ya kura mata ido, tace "ohh ashe fa hannun Yaya na ciwo ko?"
Ya kara hade rai yana harararta, tace sorry na mantane yanzu ahhhh
Fizge fork din hannunta yai yace "banaso."
Murmushi tai sannan ta sa hanunsa cikin nata tace "bakaso?"
Yanda tai maganar tare da langwabar dakai ne yasa ta kashe mai jiki, ita kanta batasan me ya sameta take wannan sakalcin ba, ko d yake dama can Jalila sakaliyace agun Goggonta.
Yace "inaso."
Yanda yai maganarne ya bata dariya ta maze tace "to In baka?"
Ganin kamar zolayarsa take tasa ya zare hannunsa yace "nama daina cin abincin tare, a samun nawa."
Ya juya baya tare da jan tiren gabansa.
Dariya tai sannan ta kwantar da kanta a bayansa tace "dani yaya?"
Idanu ya runtse dan bazai iya jurewa ba, juyowa yai ya kalleta yace "Jalila? Wato kin gama sanin lago na da alama."
Tai dariya tace "Allah yanzu zan baka Ahhh."
Bude bakin yai fuskarsa a daure ta samai tana dariya.
Kare hade rai yai yana taunawa.
************
Wani irin ihu ya saki a cikin motarsa na tsantsan farinciki, dan sai da ya zoge duka glass din motar sannan ya saki ihun tare da cewa "Kai Chairman Abubakar."
Idanu ya lumshe can ya hango sunansa a rubuce a jikin kofar office dinsa ansa *Chairman Abubakar*
Dariya ya saki tare da cewa "kai mutumin."
Tunowa yai yanda members na board din suka aminta dashi da kuma yimai alkawarin bashi matsayin Inna a jibi, zasuje company din da kansu suyi convincing din directors na cikin company din."
Wata muguwar dariya ya saki yace "kai ba sauki, kamar na janyo jibin nan haka nake ji.
Kamar ya kamata na nemi gida, dan na tabbatar matarnan tana farkawa zata nemi korata daga gidanta tunda company din na kwace.
Can kuma yace "to in ta koreni yar ta fa? Jikokinta fa?"
Dariya yai na jin dadi tare da cewa Ranka ya dade
Ina zaka?
Dariya yai sannan ya tada mota, mai makon yaje asibiti kamar yanda ya kamata kawai ya wuce gida ya shiga daki ya kwanta yana latsa waya cikin nishadi mara misaltuwa.
**************
Cikin takaici ta wanka mata mari tace "Zaliha ba kiji me nace miki bane?"
Kallanta tai shekeke tare da sa hannunta akan kuncinta tace "shine kika mareni?"
Tace "na mareki din, dan ina yayarki sai akace duk abinda kikeso a duniya sai na miki?"
Zaliha ta kumburo fuska tace "magana daya ce na miki in har kina so in cigaba da samo miki alhazawa muna amshe kudinsu, ki tabbatar kin kamomin akalar Babban yaran Taura, dan sai na kwanta dashi na nuna masa ya kwanta da trash sannan hankalina zai dawo jikina, ba sai lalai na aureshi ba."
Aunty haushi ya kara kamata tace "dalla ni rufemin baki da zancen yaran nan, sai ki dinga wani nunawa kamar fansa zaki dauka akansa alhalin ni na fahimci so kike kawai ki ganki dashi, kudi nawa kikasa muka kashe akan yaran nan da mahaifinsa? Duk abinda muka tara kinsa ya kare a shirmen banza, maza nawa ne ke sanki? Dolene sai shi? Ko dolene sai ubansa?"
Ihu tasa mata tare da cillar da pillow din dake kan kujera kasa tace "ni dai sai shi, na kuma fada miki."
Hannu tasa ta kara kifa mata wani marin tace "duk kinsa kudina ya kare akan yaran can da ubansa, bazan iya ba, ki tattara ki koma gida inyaso sai in dauko Sariha ta zo ta zauna, dama ita ta fiki san ta taho sannan na tabbatar ita bazata dinga bijeremin ba."
Ta juya tai gaba rai a bace, ihu Zaliha ta saka cikin wani irin murya tace "Aunty Aunty!"
Tanajinta ta rufo kofar falon ta fita.
"Inkoma kasarmu? A ta ina? Kasar da bakomai a cikinta sai wahala? Ni?"
(Hala ni😏)
***