tsaya a jikin katangar dakin yai shiru, ba dai yanzu opportunity bane ya bude mai bai sani ba? Kila Allah ne ya dubi zuciyarsa da yanda yai musu wahala ko shiyasa Allah ya kwantar da ita dan ya samu abinda yake so? Lalai yanzu kam ya gama sanin Allah ne yake sanshi da rahama.
Da sauri ya dau waya ya kira babban board director na company dinsu.
Yana dagawa yace "Abakar ne."
Cikin mamaki yace "Abubakar kana lfy?"
"Lfy kalau dama kira nai na fadama Hajiya ba lfy she is unconscious."
Fuskarsa dauke da mamaki yace "Subhanallah garin ya ya?"
Cikin muryar damuwa yace " wlh sai Allah, muna asibiti."
Yace "ba kanta, gashi munada meeting jibi monday."
Yace "bansan nima ya za'ai ba."
"Tunda kaine sirikinta sannan next in line ai kawai sai kai kazo."
Yace "ta inaxan zo, kamar bai kamata ba."
"Bai kamata ba kamar ya? Dama Hajiya ai ta girma akan running din company yaci ace tun yaushe tayi resigning, sai mun ganka."
Kafin Dady yai magana ya kashe.
Dady yai dariya yace "ikon Allah! Cikin sauki haka?"
Ya sake wata dariyar, hada ido suke da wata nurse sai ya wayance ya fito daga asibitin.
**********
Goggo ta shiga cikin gida ta zauna, matar babban yayansu sai kallannta takeyi.
Goggo ta kalleta tace "Yaya an wuni lafiya?"
Cikin mamaki tace "Hajiya ai ban gane bane."
Goggo tace "nice Laraban Meero (haka aka dinga kiranta lokacin tana yarinta)"
Idanu ta zaro cikin mamaki tace "inalilahi wa ina ilaihi raji'un, kece?"
Nan fa ta matso ragowar matan suka baza ido, dayar matar yayan nata ma ta taho da sauri.
Maza da suka iso daga gona kowa ya shiga mamakin jin wacece.
Goggo ta kallesu bayan sun gaisa tace "Innata fa?"
Nan akai shiru kowa na kallan dan uwansa.
Jikin Goggo a sanyaye tace "batada rai?"
Babban yayansu yace "ta rasu shekara biyar da suka wuce, har ta mutu sunanki ne a bakinta."
Goggo idanunta ya ciciko, tace "Baffa fa?"
Sukace yana kwance ba lafiya yafi shekara yana fama da ciwon ko waje baya fita."
Goggo ta kallesu nan aka shiga yi mata introducing din kowa, nan ta Nuna musu tsarabar data kawo, mamaki ne ya kamasu, ganin buhun shinkafa kwalin taliya biyu da macroni, katan din sabulun wanka guda biyar, katan din omo guda hudu, katan din sabulun wanki guda biyu, ga jarkar mangyada irin katan nan.
Nan fa aka shiga godiya da ban hakuri akan abinda aka mata, haka akai ta bata labarin yanda mahaifiyarta tai rashinta.
Goggo ta share kwallarta kafin ta shiga gun mahaifinta.
Shikam harda kukansa wajen neman yafiya agunta, yayi dana sani kara kuka ma yai a lokacin data ajiye kudi dayawa a gabansa, sannan ta fito tare da neman a rakata gidansu Abakar saboda mahaifinsa.
Sa albarka agun Baffa har ta bar dakin, mahaifin Abakar yasha kuka daya ganta, yai ta neman yafiya shima a gunsu, ta ajiye mai kudin data kawo da katan din omo da sabulun wanka tai sallama ta fito.
Bata wani zaga gari ba saboda kafarta, sai dai dakansu mutane sukaita zuwa da wanda ya santa da wanda baisanta ba, kowa yanajin tazo kawai sai dai kaga yazo.
Haka tai ta rabasu an kudi har ta samo ta baro garin....
Zuciyarta cike da tausayi da alfahari da yanda rayuwa ta juya musu....
***********
Yanda taga yana bacci hankali a kwance yasa ta zuba mai ido tana kallo, ko da wasa bata taba kawo rayuwarta nan gurin ba.
Idanunta na kansa sam batasan murmushi takeyi ba, jitai ance "zan iya bude ido?"
Mamaki ne ya kamata da sauri ta dauke ido daga kansa tare da neman dankwalinta.
Ya bude idanunsa tare da sa hannunsa ta ratsinta ya sa kansa a kasan bayanta yace " angama kallan nawa?"
Tace "wai ba bacci kake ba?"
Tai maganar tana dan juyowa kadan saboda rukun daya mata har jikinta takeji.
Fuskarsa ya dago kamar me sanyin bacci yace " kina tashi na tashi, kawai banasan farkawa ne."
Murmushi tai tace "ga alama nan, idanka ya nuna."
Matsowa yai yasa kansa akan cinyarta yana kallanta yace "idan kara kadan?"
Yanda yai maganar ne yasata murmushi tace "a nan?"
Kai ya daga tare da rufe ido yace "kinga sai ki kalleni da kyau ba takura."
Tace "ni fa ba kallanka nai........"
Fuskarta ya nuna da yatsarsa ba tare da ya bude ido ba, tace "kasa fa?"
Bai bude ido ba yace "yau Saturday kowa na gida, Ameera ma nanan."
Tace "to........"
Juyowa yai yasa kansa a cikinta wanda ya hanata magana, jitai har numfashinta sai daya amsa.
Ta kalleshi idanunsa sun firfito a hankali tai murmushi.
Hannuntantasa a cikin kansa tana mamakin rayuwa yanda ta juya musu daga ita har shi.
Kamar yasan me take tunani, dan ita ta daukama ya fara bacci sai taji yace " Jalila!"
A hankali tace "Naam!"
Yace "mu bar kasar nan."
Fuskarta dauke da mamaki tace "mubar kasar nan?"
Juyowa yai saitinta yace "Uhmm, I really want to see us alone."
Tace "nan ma ai mu kadai ne."
Sai kuma can tace "kana nufin ka yanke hukunci?"
Idanu ya lumshe mata alamar eh sannan yace "yanzun nan!"