ltan Yasmeen fa?”
Yace “tana tare da Dady.”
Bude kofar da akai ne yasa ta kalli kofar.
Safeena ce ta shigo da gudu ta karaso ta rungumeta kam, atare suka sa kuka, tare da kankame juna.
Mumy ta dagota tace “Safeena? Jiya fa mukai waya.”
Tace “Mumy dama na riga ma na sai ticket lokaci, da bakice na taho ba da wani gun zanyi.”
Mumy tasa hannu akan fuskarta tace “ya naga kin rame?”
Safeena ta share kwallarta tace “Mumy ya jikin Inna?”
Tace “gatanan sai addu’a Safeena na ma rasa ya zanyi.”
Sultan dake tsaye ya juya kansa saboda hawayenn da suka zubomai......
**************
Ihun da ake yi ana bin motar da gudu ne yasa na ruga da gudu nima dan ganin meke faruwa, kauye ne sosai dan haryanzu mota ba shiga take kauyen ba sai da dalili, dan basuda mutane masu mota.
Goggo ta kurama kauyen ido itakam bataga wani canji ba da aka samu, yana nan kamar yanda ta barshi, duk tsawon shekarun nan kuwa.
Tuno rayuwar datai a kauyen mara galihu ne yasa ta yin shiru tana bin yaran dake bin motar da kallo.
Ita da kanta ta dinga nuna layin, har suka je.
Katon gida ne na gaske amma fa ba katon da kuke zato ba, kato na yawa nake nufi.
Duk wanda zaiyi aure a cikin gidan yake zama.
Mata gasunan kacha kacha, yara kusa kamar kaje wani taron.
Ganin mota ta tsaya a kofar gidan wasu da ke cikin masu bin motar wadanda suka kasance a gidan suke suka kwalkwala da gudu gidan dan sanar musu.
Kankace me sai ga mata manya ana leka katanga dan ganin abinda ke faruwa, yara maza kuwa har sun gangara gona da gudu wasu sunyi majalisa dan kiran iyayensu maza dan suzo suga abinda ke faruwa a garin nasu.
Abba mota ya bada makekiya mai masifar kyau motar da ko a birni inkaga mutum da ita to fa lalai ya isa ne, shikansa Abba ba hawanta yakeyi sosai sai inza’ai abu mahimmi yake hawanta.
Goggo ta kalli matan dake ta lekowa ta katanga duk bata sansu ha sai guda biyu wandanda suka kasance matan yayanta maza ne.
Mamman ya juyo yace “nan ne ko?”
Tace “eh nan ne, sannu da kokari mungode fa.”
Yace “karki damu Hajiya, ki shiga kiyi abinda zakiyi a nutse inyaso da yamma sai mu koma.”
Tace “har yamma? Kai kuma fa?”
Yace “karki damu dani, zan gangara garin misau na samu abinci naci na jira ku, in kun gama sai ki kirani.”
Tace “to, ta mikamai wayar tace “ samana lambarka ko?”
Ya amsa ya saka, yai saving sannan ya nuna mata taba Lanta tace Lantana ki kalla yanda ko na kasa ganewa zaki nunamin, tace “to.”
Ta amsa ta gani sannan ta bata.
*************
Baki a sake ya tsaya yana kallan titi, me ya gani yanzu? Anya kuwa ba gizo idanunsa suke masa ba? Yanzun nan Yasmeen ke damunsa akan ice cream sun fito shiyana tunanin yanda zaiyi ya kwaci matsayin da yakeso a company dinsu, ya tsaya a gun bada hannu kawai yaga daga gefensa wata katuwar mota.
Kallan motar yai saboda kyan datamai, daidai lokacin da aka dan zuge glass din baya kadan, hakan kuma yayi daidai da bada hannun da akai, sai dai ana zuge glass din nan ya hango wata mace kai kama da Goggo, bai kara kare mata kallo ba motar tai gaba.
Kansa ya girgiza da sauri tare da cewa “lalai na fara haukacewa.”
Yasmeen tasa kuka kallanta yai yace “menene kuma?”
Ice cream dinta daya zube ta nunamai tana kuka tare da bua kafa, haushi ya kamashi yace “dan ya zube shine zaki dinga kuka haka?”
Ganin yanda yake mata fada abinda bai taba yi ba yasa ta sa kuka sosai.
Yanda yaga ana kallansa ne yasa yai saurin daukanta yana cewa “sry muje a siyo wani, shikenan?”
Kwanciya tai a jikinsa tare da ajiyar zuciya.
A ransa yace “yara duk an batasu da sakalci.”
(Nace kuma🤔?)
#OneLuv💕[12/30/2018, 9:50 PM] El-hajj: 🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
*67*
Dady yana tuki yana tunani harya isa asibitin, Mumy na zaune akan kujera kusa da Safeena tanata tambayarta rayuwar datai, jefi jefi Mumy na share hawayenta dan tausayin yarta, tace "kiyi hakuri Safeena, ni a guna gata muka miki, sai dai daga baya na gane ba gata muka miki ba."
Safeena tana kuka tace "yanzu Mumy ina Jalilan?"
Mumy ta kalleta tare dayin ajiyar zuciya na takaici tace "Jalila tafi karfin mu, tafi karfinki, yanzu tana wani matsayin da muke neman alfarma da taimako a gurin ta."
Safeena cikin mamaki tace "ban gane ba Mumy?"
Shigowar Dady ne ya hana mumy bada amsa, Yasmeen ta rugo gun Safeena da gudu tare da fadawa jikinta, Safeena ta kankameta tana hawaye.
Dady ta kalla sannan ta mike tazo kusa dashi ta rungume shi tana kuka.
A hankali ya dagata sannan yace "Saukar yaushe?"
Tace "dazu na iso shine akace su Mumy nanan muka taho da Sultan."
Ya kalli Mumy sannan yace "ya mai jikin?"
Kai kawai ta girgiza alamar ba labari.
Ya kalli Safeena yace "ki huta zanje na dawo."
Ya janyeta ya fita waje, yana fita ya