amar zatai kuka yace “kinaso na daina?”
Da sauri ta daga kai alamar eh.
Yace “tam sai kin min abu goma wanda nace inaso.”
Tace “abu goma?”
Yace “eh! A duk lokacin danacemiki inasan abu sannan na hade hannayena haka to dole kimin, kin yarda.”
Dariya tai kafin tace “lalai yaya tun daga yarintarka kakesan fanshewa, wannan fa abin yara ne.”
Yace “sosai, ai dama na fada miki ki shirya, kuka kika ce kin shirya.”
Tace “to naji.”
Bude mota yai ya fito yana Murmushi, itama ta bude ta fito tana murmushi.
Ba kowa a falo da alama kowa yana daki, sama kawai ya wuce ita kuma tai dakin Ameera.
Kanta tasa a jikin kofar tace “Ameera!”
Ameera ta taso ta bude da sauri tace “matar yaya an dawo daga hotel din?”
Tace “hotel? Nan mukace zamu dama?”
Ta dan daga mata gira tace “ai na gano.”
Jalila ta daka mata duka tace “wallahi ke yar duniya ce, uban hotel mukaje ba hotel ba.”
Ameera tasa dariya tace “wasa nake miki wallahi, kawai so nake naga na tsokaneki.”
Jalila ta harareta tace “su Ummy fa?”
Tace “sun tafi daki, ya Sageer ma haka, abincin ku na kitchen.”
Jalila tace “ai mun koshi amma bansan ko Yaya zai kara ba.”
Ta juya tace “sai da safe.”
Ta hau sama.
Hassan ya cire riga kenan tana turo kofa, kallansa tai da sauri ta nemi fita daga dakin.
Da sauri yace “Amarya ina zaki?”
Ta juyo tace “ na manta akwai abincin mu ne a kasa.”
Takowa yai inda take kawai ya maida kofar ya rufe sannan yasa hannu ya rikota.
Tace “Yaya....Abinci....”
Yace “ai kinsan a koshe muke ko?”
Tace “hmm na dauka...”
Saketa yai sannan ya koma ya dauko yar shara sharar shirt ya saka sannan yasa wando three quarter bata taba ganin ya kwanta a haka ba dan da doguwar riga jalabiya yake kwanciya.
Kallansa tai kallan mamaki, yace “ya akai? Kyau na miki?”
Tace “nagane...” sai kuma tai shiru, yace “da can ma dan karki takura ne yasa nakesa jalabiya amma dama haka nake kwanciya ta.”
Jalila tace “yanzu fa?”
Takowa yai kusa da ita, tadan yi baya kadan yace “yanzu na san mun zama daya ba maganar takura.”
Kallansa tai kawai tai yake sannan ta zauna akan kujera.
Yace “ ina kinyi sallah a gidan Goggo?”
Tace “eh!”
Yace “to ki taho mu kwanta dan bacci nake ji.”
Tace “ zan danyi tilawa ne tukunna.”
Yace “okay to ki shirya ki matso sai muyi tare, ta kalleshi kafin tace “to.”
Yaka ta shige cikin mayafi ta canza kaya cikin dabara sannan ta shiga toilet, pant dinta ta wanke ta shanya sannan tasa wanda ta shigo dashi daga falo.
Bazata manta ba a makaranta Zahra take bata labari haka taga yayarta nayi in tazo gida ko a gidanta.
(Mata ba wai sai kince ke bazaki iya wanka ba in dare yayi ba, ko kice inkinyi wanka ma miji zai saki ki sake wani, ko baki yi wanka ba at least change ur pant, wannan abu nada mahimmanci, Please karki sa pant tun safe har washegari yanada babbar illa.)
Jalila na fitowa ta dauko qur’ani sannan ta matso kusa da gadon ta hau, sai data biyamai yamata gyara inda ya dace sannan ta rufe qur’anin ta ajiye.
Jawota yai jikinsa suka kwanta, luff tai a jikinsa tanajin duminsa, a hankali taji yace “zan daure.”
Dagowa tai ta kalleshi tace “da me kenan?”
Kwanciyarsa ya gyara yace “ba komai.”
Yanda yai maganar yasa ta murmusa.
Yace “dariya kikai?”
Dagowa tai ta kalleshi tace “ni? Yaushe kenan?”
Da sauri ta maida kanta jikinsa tare da jan bargo.
Shima rufa bargon yai har kansu yana cewa “inji da kunene acemin ba’ai ba?”
Dariya tasa tace “da gaske fa Yaya ba abinda nai......”
(Jinai suna dariya nace hmm bari nai nan kafin Hassan ya fara tunanin wani abu har ya makoni......)
**************
Mumy sam ta kasa bacci daga ya dauketa take farkawa, balle dataga Inna taki farkawa, abinda likita tace mata take tunowa.
“Fatima sai dai addu’a, da yardar Allah mun samu numfashinta ya dawo sai dai bamuda ikon sawa ta bude idanunta, sai dai mu dage da addu’a sannan a kula da ita sosai, kar a dinga hayaniya a inda take, da alama wani abu mai tsananin mamaki ya faru da ita ne har yasa ta shiga shock haka.”
Mumy ta kalli Dr hankali a tashe tace “ba wani abu da ya faru da ita.”
Dr tace “ bazai yiwu ba, dan alama ce ta taji wani abu wanda ya girgizata har ya santa cikin wannan halin, karfa ki manta bawai faduwa tai ba ko kuma dama batada lafiya ne.”
Mumy tai shiru tana kallan Inna, a hankali ta goge hawayenta.
Jitai an dafata ta baya, juyowa tai ta kalleshi hawaye suka zubo mata.
Dady ya tsugunna tare da rungumota jikinsa, yana shafa bayanta alamar lalashi.
Itakam kuka kawai takeyi.
Washe gari suna zaune a asibiti wajen karfr hudu na yamma, Sultan ne ya fara shigowa.
Ajiye basket din da suka kawo kato dauke da kuloli kala kala yai sannan yace “Mumy!”
Kallansa tai tace “Su