NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 14 of 172

?" Jalila ta mike da sauri ta rike kafafun Dady tace "Dady na tuba, dan Allah kayi hakuri laifinane." Kafa yasa ya hankadata yace " gayyar tsiya." Sannan ya juya ya kalli Mumy ya dafa kafadarta yace "muje ciki ko?" Yi tai kamar me share kuka tace "Ba sai danace kayi hakuri ba?" Juyowa yai ya bugama Jalila wani kallo na takaici daga ita har Goggon sannan ya juya shida Mumy, har sun kai kofa Jalila tace " Dady me kake nufi da gayyar tsiya?" Wani banzan kallo ya buga mata sannan yace " idan kika sake min magana da wannan vibe din wlh sai jikinki ya gaya miki, sannan kiyi gagawar tasowa kiyi aikin daya kamata kiyi." Ya juya shida Mumy sukai gaba, Jalila da kallo kawai ta bisu idanunta na zubar da hawaye, kallan Goggo tai kamar zatai magana sai ta fasa, hawayenta ta share sannan ta mike ta daukoma Goggo maganinta ta mika mata tace "Goggo share kinsan halin Dady akwai saurin hawa kamar farashi, amma na tabbatar ba duk abinda ya fada yake nufi na, ai uba ubane ko?" Goggo ta tabbatar tannayi dan hankalinta ya kwanta ne shiyasa itama ta daure ta daga kai tace "haka ne." Jalila ta cire kayan makarantarta sannan ta fita. Yau kam tana aiki tana zubar da kwalla, itakam dole me gaskiya tana gama makaranta tace Sagir ya fito suyi aure ta d'auke Goggonfa subar wannan dan iskan gidan. ************ A asibiti kuwa bayan sun shiga cikin office din wanda a saman kofar naga an rubuta Neurologist, suna shiga ya mike daga zaman da yake sannan ya saki fuskarsa yana cewa Welcome Taura. Abba ya karasa kusa dashi ya mika mai hannu suka gaisa, sannan suka gaisa da Sagir, Ummy tace "Dr Ahmad mun sameka lafiya." Yace "Lafiya kalau Hajiya ya mai jikin?" Kallan Hassan tai sannan tai murmushi kawai. Guri suka samu suka zauna ita da Sagir, shi kuma ya shiga wani dan d'aki shida Hassan da Abba. Hassan ne ya kwanta akan wani abu, sai naga an tura abun cikin wani inji, da alama dai scanning din brain dinsa ake san yi, mutumin yana daga zaune yana duduba yanayin kwakwalwar Hassan. Bayan ya gama d'aukan hoto sai ya dana wani abu sai Hassan ya fito, Nan Abba yaje ya taimakamai ya sauko. Guri ya bashi ya zauna sannan shima ya zauna kusa da Dr Ahmad ya kalli Hassan yace " Hassan!" D'agowa yai ya kalleshi baice komai ba, Dr yace " kana experiencing din wasu sababbin symptoms ne?" Hassan ya girgizakai alamar a'a sannan ya dan hadiyi miyau yace " Sai dai kwanan nan bana baccin awa d'aya nake farkawa." Dr yace "da mafarkin kake farkawa?" Yace eh Bayan su fa? Yace " bakomai sai yanda dama na saba." Yace "Haryanzu kanajin numfashinka na rikewa?" Kai ya daga, alamar eh, yace " kirjinka fa? Kai ya sake d'agawa, yace rashin san hayaniya fa? Nan ma ya daga kai, Dr yace "duk ba abinda ya ragu daga abinda kake ji da?" Hassan ya d'aga kai. Dr yace " tashi kaje." Hassan ya mike ya fito daga d'akin, Dr Ahmad yai gyaran murya sannan yace "Taura abin ne sai mun dage da addu'a sannan mun bulo mai ta yanda ya kamata, da farko dai kamar yanda ka sani har yanzu ba matsala dan gane da kwakwalwarsa, matsalar tana tare ne da zuciyarsa dolene sai mun dage inhar munasan ganin ci gaba." Abba yace "Ni Ahmad na rasa yanda zanyi, abin nan ko ina muka je za'ace matsalar bata kwakwalwa bace, kuma nima na yarda da hakan, tunda yana tuka mota da kansa ba tare da matsala ba sannan bai taba yimana abu na mahaukata ba, sai dai na rasa yan......." "Abinda ya faru dashi a baya, na tabbatar shine ya rike mai zuciya, yana zargin kansa ne akan duk abinda ya faru a wannan lokacin laifinsa ne." Abba ya kalleshi cikin nazari kafin yace "amma bayan abin nan ya faru yafi shekara d'aya a asibiti ba'a hayyacinsa ba, sannan bayan ya farka akace mana ya manta da abinda ya faru dashi a wannan lokacin." Ahmad yace "That's what we think, sai dai ina tsoron kar dai abin na nan a ransa, kawai dai yana nuna ya manta ne dan neman kwanciyar hankali." Jikin Abba ne yai wani irin sanyi tsananin tsoro ya kamashi yace "Ahmad ya zamuyi?" Dr yadan yi shiru sannan yace "akwai solution, na farko ku yarda da abinda ya tsara na mantawa dayai, karka fadawa kowa tunda nima ban tabbatar da hakan ba, sai abu na biyu ina ganin ku nemomai mace wacce zata dinga kwana dashi tana yini dashi, in kuka samarmai mace mai hankali wacce zatasoshi a hankali mekin dake zuciyarsa zai warke, ko akwai wacce yake so?" Abba yace " ina ma yake kallan macen bare?" Ahmad yace "to in wannan bazai yiwu ba sai dai in sake research in dubo wata hanya, dole dai a cikin gida maganinsa yake, sannan yana bukatar kukawar dukaninku, ta hakan ne guiltiness din dake makale a zuciyarsa sai kankare." Abba yai shiru kafin can yace "na fahimta sannan duk wani abu indai har bai sabama shari'a ba zan iya aikatashi indai har Hassan zai samu sauki, domin ni da matata Allah ne kadai yasan halin da muke ciki." Ahmad yace "Karka damu Allah na tare da mu insha Allah." Nan sukai sallama suka fito, Ummy ce kawai a d'akin, Abba yace "Hassan fa?"
🏠