kam mamaki kike bani."
Ameera tai dariya tana sa turare tace "lalai Aunty Jalila ai mu nan.... a dai bar maganar kawai kar aji kunya amma idanun nan sun san komai."
Jalila tace "to kuwa na kusa fadawa Ummy ko in fadama Yaya."
Ameera tace "rufamin asiri wallahi wata kawa nai a islamiya ita ke fadamin komai, har littatafai take karanta mana."
Jalila tace "ba karatu kuke ba kenan?"
Ameera tai shiru kafin tace "munayi."
Jalila tace "Hmm..."
Da sauri Ameera tazo kusa da ita tace "Ni kaina nasan abinda muke bai daceba, kafin ma ki fada Allah na daina, dan na tabbatar Ummy inta sani zataji ba dadi dan ta yarda dani."
Jalila tace "to dan Allah adaina."
Nan suka fito tare.
*******
A falo kuwa Hassan suna shigowa ya wuce sama dan ya dauka tana can, yana shiga yaga bata ciki, juyowa yai ya fito sai daya fito falo ya tsaya yace "yanzu in na sauka bazasu fahimci abinda nazo nema ba?"
Nan ya zauna a falo na wasu yan mintina kafin ya sauko, Ummy na ganinsa ya sauko tace "Hassan ka sauko?"
Ya matso yana cewa "eh Ummy nadan shiga toilet ne."
Tace "ya kaji yau? Dakaje masallaci?"
Kusa da ita ya zauna yace "Ummy dadi, sosai."
Tai murmushi tace Alhamdulila, muje muci abinci."
Nan suka nufi dinning.
Abba da Sageer na zaune suna magana, suka karasa, Abba yace "ah mama boy an karaso?"
Hassan yace "Ummy kinji Abba abinda yake cewa"
Ummy ta kalli Abba tace " gaskiya adaina tsokanarmin yaro, haka kawai mutum da matarsa muna sa ran baby kusa amma........."
Kallan da Hassan ya mata ne yasa tace "Hmm me ma nake cewa?"
Dariya sukasa dukansu banda Hassan wanda yama rasa me zaiyi, Ummy tace "zauna kaji Hassan dina."
Hassan ya zauna yana cewa "Ummy na kula kema."
Tace "a'a ni ai wasa kawai nake ma.
Fitowar dasu Jalila sukai ne yasa ya kalli gun, dan yanajin motsi yasa tasa ce ta fito, baimayi tunanin Ameera ba dan ya dauka bata dawo ba, sannan yama manta dasu Ummy agun.
Zuba mata ido yai, wanda itama ta kalleshi, ganin yanda yake kallanta yasa kunya ta kamata, ta sauke idanunta kasa.
Sageer ne ya tabashi yace "Yaya ka manta muna falon ne?"
Juyowa yai ya kallesu yace "waccan yarinyar nake kallo, badai yau bataje makaranta ba?"
Sageer yace "taje mana sun dai tashi ne."
Fcd
Ya kalli Sageer kamar gaske yace "da wuri haka?"
Yace "ka manta friday ne? Ai da wuri suke tashi."
Yace "oh! Lalai."
Yaja baki yai shiru.
Su Jalila ne suka karaso Ummy tace "Jalila zauna kusa da mijinki, Ameera ke dawo kusa da Sageer."
Jalila ta dan kalleshi sannan taja kujera a kunyace ta zauna, itakam da kyar gaskiya ta iyacin abinci a haka? Dan ma ta yafa mayafi a kasan kafadarta.
Ameera ta karaso ta gaida kowa, ita ma Jalila ta gaishesu, Hassan kam kallanta kawai yai bai ce komai ba.
Abba ne ya fara zuba abinci kafin kowa ya zuba, Hassan bai kara kallanta ba sai dai gaba daya so yake a dan tashi su hau sama kawai ya dan jawota jikinsa ya rungume.
Haka kowa ya zuba itakam dan kadan ta zuba a plate dinta, Hassan dayazo zubawa ya jawo plate dinta ya kara mata, a hankali cikin maganar rada yace "ko kinfisan ci da ni?"
Kallansa tai sannan tai kasa dakai, tura mata plate dinta yai sannan ya zuba nashi ya ajiye.
Duk abinda sukeyi kowa na kallansu amma ba wanda ya bari aka gane, a hankali take cin abinci, har ya kusa cinye nashi bata wanici dayawa ba, Hassan ya karkato kadan yace "in ba so kike na baki a gun nan ba kiyi gaggawar ci."
Tace "inafa ci?"
Yace "to ko na taimaka miki kici sosai?"
Da sauri tace "zanci."
Murmushi yai sannan ya juyo, Sageer? Abinda ya fado mai kenan da sauri ya kalleshi, gani yai hankalinsa ma baya kansu, magana suke da Ameera.
Gaskiya shikam yana tunanin barin gidan nan, ko saboda Sageer kamar bai mai adalci ba, gwara ace suna dan nesa ko yaya ne.
Abba ne bayan sun gama suna shan fruit din da suka kawo a falo, Jalila da Ameera na zaune a gefe, ya kalli Hassan sannan ya kalli Ummy yace " jiya inata wani tunani."
Tace name kenan?
Yace " akan karatun Hassan, kinsan yanda kasarmu take, yanzu in Hassan zai nemi level 1 duk abin baxai mai dadi ba saboda shekarunsa, shiyasa nake tunanin mu nemarmusu kasar arab haka suje can shi da matarsa suyi karatunsu a tare."
Hassan ne ya kalli Abba yace"Abba wata kasar?"
Yace "Eh mana ai gwara a nema tun yanzu kafin karfina ya tafi, yanzu ga Sageer kaga inka dawo kuka hadu ku biyu hankalina zaifi kwanciya nima sai na ajiye aikina na huta."
Ummy tace "kace jiya bakai bacci ba kanata tsare tsare?"
Yai dariya yace "kudaije kuyi shawara ku gani dakai da matar taka."
Hassan yace to, yanasan barin gida amma ba wata kasar ba.
Mikewa yai ya hau sama, Jalila ta bishi da kallo, Ummy ce tace "La Jalila kinga baisha abarbarnan ba, dauka ki kaimai."
Tace to sannan ta mike tazo ta dauka tahau sama.
A hankali tasa hannu ta murda kofar tare da sallama, Hassan na zaune a bakin gado ta shigo, drawer dake gefen gadon da