a dinkinta yake?"
Tace "wlh ban sani ba Ummy, na daiga shine a sama."
Ummy ta mike tazo ta bude kayan, maidasu tai ta cigaba da dubawa, sai datazo kan wani material mai masifar kyau, jikinsa kamar lace yake sai dai ba kafe bane, ita tasiyoshi da kanta sanda ake hada lefe.
Budeshi tai taga dinkin kuwa yayi kyau riga da skirt ne.
Ta ajiye sannan tace "muje?"
Jalila tace to, Ummy tace "dauko inners."
Kunya ta kama Jalila ta zaro ta cusashi tsakiyar kaya, Ummy tace "mu tafi to."
Nan suka sauko Ummy na rike da hannunta.
Da yake toilet din sama bashida bath hub kawai gun shower ne aka killaceshi shi yasa ta sauko da ita.
Dakin Ameera ta kaita sannan ta shiga toilet ta kunna ruwan zafi, sannan ta toshe makwararar ta fito, zama tai kusa da Jalila wacce ita gaba daya ta kasa gane me Ummy ke nufi, ba dai tasan wani abun ya faru ba? Ko da yake bata fada ba ta ya zata sani?
(Nace uhm yaro man kaza🤣)
Fita Ummy tai bata dade ba ta shigo rike da kofi, na baza ido ina san ganin menene a ciki, mikama Jalila tai tace "sha."
Jalila ba musu ta amsa ta kafa kai ta shanye, sannan ta mikama Ummy kofin, Ummy ta kalleta tace "Munyi waya da Goggonki tace "tanaso tadan je kauye taga gida."
Jalila tace "jiya munyi waya amma bata fadamun ba."
Ummy tai dan dariya kafin tace "batasan ne kece sai kin bita."
Jalila tace "Amma Ummy ba tare ya kamata muje ba?"
Tace "tunda dai ita kadai take san zuwa yanzu sai ki barta taje inyaso ke daga baya sai kije ko da Hassan ne ko kuma ku koma tare."
Jalila ta daga kai alamar to, sannan tace "yaushe zata?"
Ummy tace "gobe da safe, nasa Sageer ya tura Mamman driver da mota sai suje tare."
Jalila tace "to Ummy Allah ya kaimu, mungode sosai."
Ummy tace "muma mun gode, ta shiga toilet, sai dataga ruwan yayi kusan rabi sannan ta kashe ta taba ruwan, jun zafi sosai yasa ta kunna na sanyi.
Sai data tabbatar komai yayi sannan ta fito ta kalleta tace "ki shiga cikin ruwan ko zuwa minti 20 ne zakiji dadi inkin fito."
Yanzu kam Jalila ta fara fahimta, da sauri ta sunkuyar da kai cikin kunya, Ummy ta juya ta fita.
Jalila kunya ta rufeta da kyar ta mike a shiga.
Yanda Ummy tace tayi haka tayi.
Ta dade a ciki kafin ta cire tai wanka.
Taji dadin jikinta sosai, kaya ta saka ta shafa mai da powder sai turare kawai ta fito falo.
****************
Zaliha ce ta shiga wurgi da kayan dake cikin wardrobe dinta tana wani irin ihu, Auntyn ta ta matso tana cewa "Zaliha menene hakan wai? Tunda kika dawo daga kano gaba daya kin koma kamar wata wacce bata cikin hayyacinta, wani abun ya faru ne wai?
Kayan kawai take zubarwa tana ihu, ganin abin yaki karewa yasa ta matso kusa da ita ta rike hannayenta, ta girgizata tace "Zaliha wai meke damunki? Gaba daya kin canza, ko abincin kirki ba ci kike ba, wai menene ke faruwa? Kin ki fadamin sai ihu kawai kike."
Ture Aunty nata tai ta fada kan gado tace "me? In amince duk abinda nakeso zan samu? Kinsan me aka kirani dashi? Ko bacci nakeyi in na tuno abinda akamin sai dai na farka, ko abinci nasa abakina ina tunowa sai naji bazan ita taunawa ba."
Tace "to me aka kiraki dashi?"
Kara watso wasu kayan tai wanda suka rage a ciki ta sa wani ihu na bakin ciki......
Mamaki da tsoro ne suka hanata magana, tana kallan yanda take ihu daga baya ta tsugunna kawai tasa kuka.........
**********
Yana isa yai parking ya fito da sauri dan ganin motarsu na kokarin fita, wayarsa ya dauko da sauri ya kira number Abba, Abba ya daga yana kallan Sageer.
Hassan yace "Abba gani nazo, naga kamar zaku fita."
Ya kalli Sageer ya fadamai, nan Sageer ya juya kan motar, a tsaye suka ganshi, suna karasowa kawai ya shiga bayan motar.
Abba yace "motar taka fa?"
Yace "in mun dawo sai in biyoka sai na dauka, ko na turo mamman."
Abba yace "okay, dan daga masallaci gida zamy muyi lunch."
Sageer ne ya juyo ya kalleshi yace "Yaya barka da isowa."
Hassan ya kalleshi cikin tsantsar kulawa yace "ya? Ko na anshi tukin ne?"
Sageer yai dariya yace "yaya ka manta? Na rigaka fa iya mota, kai da sai da daga tasa ka gaji da zaman daki kasa Mamman ya koya ma."
Hassan ya harareshi yace "amma dai daga nan har......"
Abba yai dariya yace "ba wani har..... shi dai mutun tunda an wuceshi shine yake neman waskewa."
Hassan yace "bakomai tunda hademin kai za'ai zan sanar ma Ummy na nima."
Sageer yai dariya yace "wai yaya wallahi Allah ne kawai ya tsare da katon Mama Boy za'ai."
A tare suka sa dariya da Abba, Abba yana cewa "sosai ma."
Hassan yace "to duk kowa ya gama nima zan fanshe."
Haka sukai ta yan tsokana kana ganinsu kaga mutanen dake cikin tsantsar farin ciki, bazaka taba tunanin wani ba dan wani bane a cikinsu.....
(Ni kaina da badan Hassan ya sanar ma Jalila ba ko da wasa ban taba kawo hakan ba.....)
#OneLuv💕
[1/12, 9:39 AM] Maryam: 🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
_Gaisuwa gareku yan Maryam Salisu Maidala, Hausa Novels Room, Unity Girls 2011, Mamu No