a'a magana.
Tana tafe tana dan mitocinta ita kadai..........
************
Inna ce ta kalli Sani sannan ta kalli takardar daya kawo mata dauke da sunan Taura da number sa.
Tace " da ka sake bincike ba wani abu game da rayuwarsa da ta kyalansa bayan matsalar yaran?"
Sani yace "eh gaskiya ba wani abu special, sai...."
sai kuma ye " ba ma dai komai."
Tace "da ke zaka fada?"
Yace dama kamar yaransa maza biyu ne, 'yan biyu babban Hassan sai kaninsa Husaini, sai dai jiya sai aka cemin wai Hassan ne da Sagir sai macen.
Inna tace " ko dai kaine ka manta ba?"
Yace "zai ita yiwuwa inaji Husainin tun yana karami ya rasu."
Tace " Dama ai maza biyu mace d'aya kacemin."
Yace "hakan na sani amma nadauka 'yan biyun ne ashe wa da kani ne."
Inna ta jinjina kai cikin rashin damuwa tace " ba wani abu bayan nan?"
Yace "babu."
Nan ta saka number a wayarta sannan ta anna dialing.
Sai atai ringing hudu sannan ya d'aga.
A banngarensa yana zaune a bayan mota shi da Ummy, sai Sagir dake zaune a mazaunin driver shi kuma hassan na gefe, suna hanyar zuwa asibiti.
Yana daga wa Inna tai sallama,Abba ya amsa sannan yace "ban gane ba."
Inna tace " Taura nice Hajiyar grain."
Sai daya danyi nazari na wasu dakiku kadan sannan yace "Hajiya ina wuni?" Yai magana tare da canza yanayin maganarsa zuwa girmamawa."
Inna ta amsa sannan tace " Taura ganinka nake san yi ina fatan zaka bani lokaci."
Yace " Haba Hajiya, kina wani gari ne?"
Tace ina kano, ina neman alfarma ganinka sanda kake da lokaci.
Yace " yau dai inada abinyi, sai dai banaji gobe akwai abinda zanyi, a ina zamu hadu?"
Ya fada yana kallan Ummy, tace " gida na zakazo ko nice zanzo ko kuwa a wani gurin zamu hadu?"
Yace " a'a ba matsala ni zan zo."
Tace "Nagode Taura zan turoma da address din gidan."
Ya amsa da to sannan ya kashe wayar, Hassan ya kalla wanda idanunsa ke rufe kamar me bacci sai dai kowa na cikin motar yasan ba bacci yake ba, Ummy ya kalla ya shiga fada mata wacce ta kira.
Gate din wani katon asibiti naga an bude musu, Sagir ya shiga da motar.
*************
Jalila kam taci uwar tafiya kafin ta isa gida, duk ta gaji tayi ligib.
Tana shiga ta tadda Mumy a bangarensu, gabanta ne ya fadi sannan ta kalli Goggo wanda kuka ne kawai batai ba amma da alama daurewa kawai takeyi.
Mumy na ganinta tace "kin dawo daga yawon iskancin?"
Jalila fuska ta canza sannan ta kalli Goggo wacce ta tabbatar an kare mata cin mutunci ne, tace " Mumy ban gane b....."
Marin data kifa mata ne yasa ta kasa karasawa sannan ta rike kuncinta, Mumy tace " ce miki akai nan gidan karuwai ne? Ko me?"
Mamaki ya kama Jalila tace " Mumy ban ga........."
Wani marin ta kara kifa mata tace "a gidan ubanwa kika tsaya? Kungurmar munafuka? Dama kwanakin nan na kula bakyasan dawowa tare dasu Safeena saboda kina yawon bin maza."
Cikin wata irin kakkausar murya Goggo tace " RAMLATU!"
Kallan Goggo sukai a tare, dan Jalila bata taba ganin ran Mumy ya baci ba haka.
#ONELUV💕
[08/10, 19:18] +234 816 365 0557: 🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *AyusherMohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*NO 7*
Goggo cikin jin zafin kalaman Mumy tace "Ta ya zaki kira yarinya ta da haka? Kina tunanin 'ya'yanki sunfi na wa ne? A koda yaushe ina jure komai ne badan banajin zafin abinda akema Jalila ba sai dan ina tunanin kila hakan shine zai kawo salama a zuciyarta, komai da kika gani inayi inayinsa ne domin ta, taya ma zaki kalli 'ya a gaban uwarta ki kirata da wadan nan munanan kalaman?"
Mumy ba shakka ta dan tsorata, ta daure tace " ni kike yima fada? Kijira ni."
Tafada tare dayin waje da sauri, tana fita Goggo ta rike kirjinta wanda ya mata wani irin nauyi, ga wani irin dum na tsananin ciwon kai daya fara sara mata, Jalila ta karasa kusa da ita tare da rungumeta tace "Goggo na."
Cikin shagwaba tai maganar, Goggo ta daure dan batasan Jalila ta gane batada lafiya tace " Karki damu, ko me za'amin indai har akanki ne zan ita jure komai."
Jalila ta kwantar da kanta akan kafad'ar Goggo cikin tausayama kansu.
Banko kofar da akai ne yasa ta d'ago da sauri cikin tsoro, Dady ta gani bayansa Mumy ce.
Jalila da sauri ta mike ta tsaya a gaban mahaifiyarta alamar kareta tace "Dady kome ya faru laifi......."
Wani wawan mari daya kifa mata sai data fadi kasa, Goggo ta d'agota da sauri tana tambayarta.
Dady cikin tsananin bacin rai ya kalli Goggo yace "uban wa ya baki dama ki cima matata mutumci?"
Goggo ta kalleshi tace " ni duk mutuncin data cimin bai zama laifi ba kenan?"
Yace " Me yasa bakya abu da tunani? Ko kuwa kwakwalwarki ce bata aiki? Gidan da kike zaune,abincin da kike ci, kayan da kike sakawa, karatun 'yarki duk a cikin arzikin wa kike ci?"
Goggo tai shiru tare da maida kanta kasa, sannan tace " duk da haka banaji tanada damar cima 'yata mutunci...."
"Yanzu yarinya tayi laifi kina nufin tafi karfin a hukuntata ne ko me