ta sa number ta juya ta fita.
Ameera na san magana amma ba dama, saboda ta fahimci sabani suka dan samu.
Jalila na fitowa ta koma sama ta zauna a bakin gado rike da waya a hannu.
Ta zarfafa cikin tunani taji wayarta na kara, da sauri ta dauka ko kallan mai number batai ba tai sallama.
Goggo tace "Jalila!"
Cikin mamaki ta kalli number sannan tace "Goggo? Number wanene?"
Goggo tace "tawa ce, yanzun nan aka aikon da ita."
Tace "wane?"
Tace "ai ke zan tambaya,tunda haka akacemin gashi daga Jalilah, na dauka ma number ce baki sani ba."
Jalila tace "bansani ba wlh,amma nasan bai wuce inji Ummy."
Tace "kila to, ya gidan naku?"
Tace "lafiya kalau inatasan nima nazo."
Goggo tace "a'a banasan yawon zuwan nan ba dadi, ke dai ki zauna a gidanki cikin iyalanki, ni muna zaune da Lantana lafiya anan, komai muna dashi, a koda yaushe sai dai in muku addu'a dake da mutanen nan na arziki."
Jalila tai murmushi sanda ta tuno Hassan a ranta tace Goggo ina cikin wani hali.
Amma a fili tace "to Goggona."
Nan sukai yar fira kadan kafin suyi sallama, Kara kallan wayar tai tana tunani, idanunta ta rufe sannan ta mike tai alwalar magrib tai sallah ta kara dauko wayarta, yanzu kam kiranshi tai sai dai bai dauka ba harta katse.
Shi kuwa Hassan tunda ya fita yake tafiya a mota, yayi tafiya mai tsawo kafin ya ja gefen titi yai parking? Kansa ya kwantar akan kujera ya rufe idanunsa, da wani irin zama zasuyi? Ya tabbatar akan wata alaka a tsakaninsu mai karfi, yanda ta razana, idanunta ta ya tuno da yanayin da ta shiga a lokacin, kenan har yanzu tanasan Sageer?
Idanunsa ya runtse cikin wani irin hali, yana ganin kiranta bai dauka ba har ta gaji ta daina.
Ummy daga kasa taga ba Jalila gashi har lokacin cin abincin dare yayi, Ameera ta aiko akan ta kirata, lokacin tana kwance akan sallaya, Ameera ta turo kofa tana lekowa tare dayin sallama a hankali, Jalila ta kalleta tana ganin ita kadaice ta shigo.
Ameera tace "ki sauko muci abinci, yaya fa?"
Jalila tace "nakoshi, sai dai bari sauko na daukomai nashi."
Ameera tace "kinsan sai dana bude kofar na shiga tunanin in yaya na nan fa?"
Hmm kawai Jalilah tace batace komai ba, ta mike suka sauko w AUmmy tace "bai dawo ba?"
Tace "eh Ummy inaji ya tsaya a wani gun ne bari na daukar mai."
Ummy ta dauka su biyun take nufi, shiyasa batace komai ba.
Kitchen ta shiga ta zuba mai sannan ta dau tiren ta fito, tana shigowa falon Sageer da Ameera na fitowa daga daki, da alama kiransa taje yi.
Gaisheshi kawai tai ta wuce sama tareda yima Ummy sai da safe.
Ta hau sama, abincin kawai ta ajiye tai sallar isha'i sannan ta dauko qur'ani inda ya koya mata jiya ta biya sannan ta dawo farko, ta dade tanayi kafin ta rufe qur'anin tadan kishingida tai akan sallaya, bacci ne ya dauketa.
Sai can wajen karfe 11 ya dawo, yana shiga ya shiga toilet ya fito ya kwanta.
Juyi ya shiga yi, hankalinsa bai kwanta da kwanciyar datai a kasa ba, gashi ba bargo, duk yanda yaso yai bacci ya kasa.
Mikewa kawai yai yadau bargo ya rufa mata ya koma ya kwanta.
Da asuba yana sallah yau ko karatun bai koya mata ba taga ya juya ya kwanta.
Dama tashin ma sai data farka taganshi kawai yana sallah.
Tace "Yaya ba....."
Yanda ya kwanta yasata yin shiru dan bashida alamar sauraranta.
Tama rasa me zatace, haka ta gaji ta kwanta.
Tana tashi taga baya dakin.
Gaba daya hankalinta ya kara tashi, ta fito falo ta zauna idanunta suka ciciko, batasan ta damu da Hassan ba kamar yanzu, gaba daya kin kulatan dayai na kwana dayan nan jitake kamar tayi hauka, me yasa Yaya bazai bari tayi magana ba?
Shikam gaba daya bayasan yaji wani abu daga gunta, tsoro yake kar tacemai Sageer takeso ba shiba, dan bayaji zuciyarsa zata dauki wannan hukuncin, a yanzu bayaji zai iya rayuwa ba Jalilah, to in itama bazata iya rayuwa ba Sageer bafa? Ko shi yace bazai iya rayuwa ba ita fa? Wannan dalili yasa yake tsoron jin abinda zai fito daga bakinta.
Wajen karfe 8 ta farka, da sauri ta bude dakin sai dai ba shi ba alamarsa, abincin daren ta kalla, ta bude kulolin, gaba daya ba alamar ma ya bude shi.
Kawai zama tai a kasa tasa kanta a cikin cinyoyinta, samun kanta kawai da sa kuka, yanzu inyace yabarma Sageer ita fa? Dan ta kula gaba daya ba wanda yake damuwa da ra'ayinta dukansu tunanin junansu kawai sukeyi.
Haka ta sauko da abincin, tai sa'a Ummy ma sun fita da Abba, tana fitowa Sageer ya sanar da ita, Ummy ta riga hartayi abincin safe, komawa tai sama kawai ta kwanta dan bazata ma iya cin abincin ba, tai wanka tasa atamfa riga da skirt kawai ta murza mai da turare ta kwanta.
Wayarta na hannunta jefi jefi tana kokarin kiran Hassan.
Sai wajen rana ta sauko tai abinci kawai tasa a kula ta koma sama.
Yauma bai dawo ba sai data kwanta barci, ya dade a tsaye yana kallanta, sannan ya kalli abincinsa data ajiye masa, zuciyarsa na tsoron jin labarin nan, jiyake bazata iya daukan abinda zata ji ba.
Bargo ya dauka kamar jiya ya l