gaba daya haka rayuwata take a cikin wannan gidan nasu, komai sai abinda suka tsara, basu dauke da girma ba duk kuwa da nine mahaifin yaran.”
Ya kara neman marairaicewa zai kara wani rainin hankalin Ummy ta shigo falon dauke da ruwa da juice.
Wannan dalilin ne yasa ta yin shiru, tana kallan yanayin Abba ta fahimci baya jin dadin hirar, sai tai sa’a kuwa tana fitowa sai ga Jalila.
Dady ya kalleshi ya sake marairaicewa yace “a koda yaushe sai sun yanke hukunci nake sani, sannan ban isa na kawo nawa uzurin........”
Sallamar Jalila ce ta katseshi, haushi ya kara kamashi.
Abba kam yana ganin Jalila ya mike tsaye yace “bari na barku ku tattauna.
Dady ya mike da sauri yana cewa “Danka ya dade......”
Ai Abba bai jira cigabansa ba yai waje, yana fita yaja wani dogon tsaki ya kalli Ummy yace “wlh dabadan mahaifin Jalila bane da wlh mutumun nan...” sai kuma yai kwafa.
Ummy tai daria tace “ni ina kallanka nasan ha labari.”
Ya kalli kofar yace “mutum na kara banzatar da kansa da wulakanta kansa saboda abin duniya?
Dady kallan Jalila yai bayan ta shigo ta tsugunnadaga can bakin kofa.
Yace “Jalila! Ya da zama daga nan? Nine fa mahaifinki, yanzu in wani ya shigo ya ganmu ai dauka zaiyi wani abin nake miki, taso dan Allah.”
Kallan mamaki tamai, sannan ta mike ta taso, zaka tai daga gefensa kadan matso da jikinsa inda take, yace “Jalilah!”
Dagowa tai ta kalleshi sannan ta gaisheshi, ya amsa fuska a sake kamar wanda akayima wani gagarumin albishir, Dady ya kara sakin fuska yace “ya jikin Goggon taki?”
Kallansa ta sakeyi tace “da sauki.”
Yace “Jalilah!”
Ta kalleshi sai dai fuskarta ba a sake ba, tace “naam”
Yace “Jalila ni mahaifinki ne wanda nine na haifeki, nafi kowa sanin zafinki da darajarki, koda duk mutanen duniya zasu kike wallahi ni bazan taba gudarki ba.”
Jalila batasan sanda ta juyo ta kalleshi ba cikin mamaki take kallansa.
Dady yace “ki dainamin kallan tantama sai dai nidin da gaske nine na haifeki, jinin jikinki daga jikina yake, amma nikam Jalilah kinji wani abu na harkar company dinmu a nan gidan?”
Yanzu kam zargin da take ta gama tabbatarma kanta, ta daure tace “kamar name kenan?”
Dady ko kunya yace “ dama inata tunani ne ko da yanda za’ai tunda dai yanzu kudin sirikanki ne gaba daya yanzu yake tafiya da company din me zai hana ki taimaka ki sanar dasu a bani company din, ni nafi kowa sanin darajarsa, lokacin kankani zan maida musu kudin su, na tabbatar bazan taba basu kunya ba.”
Jalila kallan mamaki kawai takemai, baijira tama kaiwa kwakwalwarta amsar da zata fadamai ba taji yace “Jalila har zuciyata banasan rabuwa da mahaifiyarki, in har suka takura sai na bar musu gidan kawai, muzo muyi rayuwarmu daga ni sai mahaifiyarki, sai ke inkinzo.”
Jalila yanzu kam ta kai matuka gun tunzura wato itace kuka mai dadin hawa kenan itada mahaifiyarta, shiyasa yazo mata da wannan zancen?
Ta kalleshi ta tuno kalaman Hassan tace “Dama ko da wasa nasan wallahi Dady bazaka taba zuwa saboda ni ba, ko goggo.”
Ya kalleta yace “bangane ba?”
Tace “yanzu Dady wani mahaifine zaiyiwa matarsa haka? Wani mahaifine zai nemi saida yar sa amma daga baya ya dawo ya nemi kara saida nasa mutunci?”
Cikin tsananin bacin rai yace “Jalilah? Bakida hankali? Ni kike..........” sai kuma ya canza tone din maganarsa yace “Nine na haifeki ba wani ba, nine jininki.”
Hawaye ne ya zubo mata tace “jini? Dady sai yanzu kasan jini? Sanda ni da mahaifiyata muke kuntata muke neman tallafinka, Dady kana ina? Kana ina lokacin da.........”
Hawayene yacikarfinta, ta kasa karasawa, Dady ya turzuko yace “bakin ciki kikemin? Bakin ciki kikeyi zaki taimakeni?”
Jalila ta kalleshi cikin takaici tace “bakin ciki kamar ya?”
Yace “inba bakin ciki ki...........”
Bakin ciki take maka, ko dole ne dan ka haifeta sai ya zama dolene duk wani abu daka zarta mata sai ta bishi?”
Juyowa yai da sauri, saboda muryar dayaji, a tsorace ya mike tsaye ya kalleshi.
Hassan wanda har ya zauna yai tunanin kamar ya dace yazo ya gaida shi, yana tsaye Dady ya fara mata zancen karshe da amsar data bashi, dan dama yana fitowa daga wanka riga ya zura kawai ya sauko.
Dady ya kalleshi yace “Hassan ba.......”
Hassan yai saurin cewa “bansan me ka ke nema a gunta ba, na dauka bayan neman saida ita dakai bakada idan neman wani abu daga gunta, amma yanzu na gane duk ba haka bane, tun farko zuciyarka dama ba komai a ciki sai tsantsar san kai, in ba kanka ba banaji akwai abinda kakeso a ciki.”
Dady ya fara kokarin yin magana, Hassan ya matso ya kama hannun Jalila yabar falon da ita.
Dady ya tsaya sakato, cikin kunar rai.
Hassan kam janta kawau yakeyi, ya matse mata hannu har sai da suka shiga daki, ransa ya gama baci ya kalleta yace “sau nawa zance ki zama mai confidence?”
Kanta ta karkatar tana kallansa, a hankali ta saki murmushi ta