Sageer ya matso ya masa bayani, ai bai bi takan Sageer ba naga ya sauko da sauri ya dau key din mota ya fita "Ummy ina zuwa" abinda ya fada mata kenan a sanda ya ganta a zaune.
Kafin ta amsa masa yafice, tad'anji zanyi aranta, tunda yau ga Hassan zai fita harda fad'in yana zuwa, tamance shrkarun daya d'auka bai Sanar mata zai fitaba.
Sageer na saukowa yaga har ya ja motarsa ya fita, motarsa shima ya shiga yana tunani, ya bishi ne?
Can kawai yaja motar sa shima ya fita.
***********
"Alhajina kayi shiru, kobakayi murna da ganina baneba?".
Abba ya had'iyi yawu da k'yar, kafin yace, " bahaka baneba zaliha, kawai nayi mamaki. ganinkine, musamman idan anyi la'akari da safiyane, dolene kayi mamakin ganin Wanda yake Abuja a Kano a irin wannan lokacin".
Cikin salonta Na yaudara tace, "Alhajina kamanta da maganarnan ta Malam ba haushe dayace garin masoyi baya nisa........
.......baya nisa kam, balle idan kaci karo da ballagazar mace, wadda batasan muhimmancin dunk'ulalliyar zuri'a ba, narasa wane rukuni zan sakaki acikin jinsin d'an adam....."
Daga Abba har Zaliha a rikice suka juyo suna kallonsa.
Bakowa baneba face Hassan.
Yauce rana tafarko daya taba shigowa company d'in Abba ballema office d'insa, dukda yasan inda company d'in yake, amma yanzuma bisa jagorancin Sectary d'in Abba yazo, yanaji ajikinsa dama wataran sai zaliha tabiyo sawun Abba tunda batasamu yanda take soba.
Sai gashi kuwa, tunkafin ayi nisa saigata tazo d'in, hasashensa yazama gaskiya.
Bak'aramin tashin hankali Abba yashigaba, hakama Zaliha dake zaune, dan sarai tagane Hassan d'in, shine taga hotonsa a wayar Taura shida k'aninsa, tun ama hoton ta shaida wannan guy d'in bazaiyi mutunciba, balle tundaga waya dashi Taura ya dauke mata kafa.
Hassan yakatse mata tunani da fad'in "Bakiji gargad'in dana miki bane ko kuwa wanda na miki ne ya miki kadan?
Zaliha ta kalleshi idanunta suka firfito, a hankali ya fara takowa har inda take yace "zaki sauko daga inda kike zaune ko inzo in saukeki?"
Da sauri ta cire hannunta daga jikin Taura ta sauko daga kan desk din, wani kazamin kallo ya mata yace " fita fa? Zaki iyayi ko sai na jaki daga nan har waje?"
Kallan Taura tai tace "MyT?"
Taura ya kalleta ya dake yace "ke karki kara cemin wani urT agidan uban wa na zama naki?"
Juyowa tai jiki a sanyaye ta fara takowa, kusa dashi tazo ta tsaya tana kallansa, tare da dan girgiza kirjinta.
Tsaki yai yana kallanta yace "kina tunani wai kin cika mace a hakan?"
Tace "mene?"
Bai bata amsa ba yace "kinsan wani suna ake kiran mata irinku?"
Tace "mene?"
Nan ma bai bata amsa ba yace "kinsan a wani jere nake sa mata irinku?"
Haushi ya kamata tace "mene?"
Yace "Trash! Get out."
Idanunta ne suka firfito fuskarta ta nuna tsananin bacin rai ta kalleshi tace "mene?"
Yace "bakyajin turanci?"
Kallansa ta sakeyi cikin wani yanayi na tsananin bacin rai, cikin mumunan bacin rai ta fito.
A waje taga Sageer a tsaye a jikin kofa, kallansa tai yai dariya har tayi gaba yace "ke Trash kin manta jakarki."
Yafada tare da kallan jakarta dake kan desk.
Dawowa tai ko kunya ta dauka ta fita da sauri.
Sageer ya bita da kallon mugunta, ya kalli Hassan yace "kai Yaya baka zafafa ba?"
Hassan yace "kaima ka zafaffa ai wai ke Trash...."
Abba ne ya hade fuska yana kallansu yace " wato dai kune masu kula dani ko? Sai a fadamin wanene ma ya samar daku?"
Hassan ya kalli Sageer, da sauri Sageer ya juya kai yace "Abba na manta inada appointment" dariya suka saka a tare hardashi Abban, Abba yace "amma yanzu ai bazata sake dawowa ba ko? Sageer yace "inta dawoma tana da mai maganinta....
Suka kara yin dariya.....
Abba yace kuyi alwala muje masallaci sallar la'asar tare.
Hassan ya kalleshi, Abba yace "let us try kaji?"
Ya daga kai alamar to.
Haka suka yi alwala suka zauna a office din Abba macema Sageer ya daure ya fara aiki anan, Hassan na taya Abba har la'asar ta karasa, Abba ya kalli Hassan yace "muje?"
Atare suka fito su uku abin sha'awa, basuga motar Zaliha ba agun da alama ta bar gun.
Masallacin suka nufa, tsayawa yai yana kallan yanda mutane ke ta shiga ciki, ya kalli Abba.
Abba yasa hannu ya riko hannunsa sannan ya riko hannun Sageer yace "gamunan mu uku, ka cire komai a ranka kawai kasa a ranka gun bautawa Allah zaka, sannan gamu a kusa dakai."
Hassan yai murmushi suka nufi masallacin, daurewa kawai yake dan zuciyarsa sai bugawa take da sauri da sauri.
A bakin kofar suka tsaya sukai addu'a sannan suka shiga.
Haka suka shiga, suna shiga ciki suka hau jam'i a tsakiya suka sakashi, liman yaja sallah.
Suna idarwa Abba ya kalleshi, wasu zafaffan kwalla ne suka shiga neman zubomai a lokacin daya daga hannu yana rokon Allah, yaushe rabo? Addu'a ya shiga yi har bai san sanda hawaye ya zubo mai ba.
Sageer ma sai daya zubo da kwalla saboda tsananin tausayi.
Ya dade yanata addu'oi kafin su fito, dan sukan shi suka ts