NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 124 of 172

ya kalli Abba. Abba yasa hannu ya riko hannunsa sannan ya riko hannun Sageer yace "gamunan mu uku, ka cire komai a ranka kawai kasa a ranka gun bautawa Allah zaka, sannan gamu a kusa dakai." Hassan yai murmushi suka nufi masallacin, daurewa kawai yake dan zuciyarsa sai bugawa take da sauri da sauri. A bakin kofar suka tsaya sukai addu'a sannan suka shiga. Haka suka shiga, suna shiga ciki suka hau jam'i a tsakiya suka sakashi, liman yaja sallah. Suna idarwa Abba ya kalleshi, wasu zafaffan kwalla ne suka shiga neman zubomai a lokacin daya daga hannu yana rokon Allah, yaushe rabo? Addu'a ya shiga yi har bai san sanda hawaye ya zubo mai ba. Sageer ma sai daya zubo da kwalla saboda tsananin tausayi. Ya dade yanata addu'oi kafin su fito, dan sukan shi suka tsaya jira, dukansu sai tausayinsa yakeyi. ^********** Dady ne ya kalli kofar gidan, kwanansa biyu kenan yana zuwa yana komawa dan shifa gaskiya ya kasa sa kafa cikin gidan, ko dai wayau zaiyi ya fara zuwa gidan da Goggo take? Ita yasan mai sauki ce inyaso sai tazo nan da kanta ta basu hakuri..... Juyawa yai da motar kamar zai koma sai ga motarsu Abba. Kallansu yai sun shiga ciki, sun hada ido da Hassan amma sai ya dauke kai, da kallan takaici ya bishi yace "wannan dan iskan yaran....." Suna shiga shima ya shiga da motarsa. Su Abba na fitowa shima ya fito da sauri yace "Ranka ya dade!" Abba ya juyo ya kalleshi, murmushi yai yace "Ah Alhaji kai ne?" Dady ya matso yana kallan Sageer da Hassan da sukai kamar basu ganshi ba. Hassan ya kalleshi bayan ya karaso yace "Ina wuni?" Dady ya washe baki yace "Hassan an wuni lafiya?" Hassan yace "lafiya." Ya wuce ciki, Sageer ma yace "Ina Wuni?" Nan ma yace "malam Sageer ko?" Sageer yace "eh." Ciki yai Abba yace "bismillah!" Nan suka shiga ciki........... Falonsa ya kaishi ya zauna sai wani washe baki yakeyi, yana cewa "wlh na dade inasan nazo." Abba ya kalleshi baice komai ba..... Shiru sukai dan Abba kam shikanshi haushinshi yakeji, ai koda laifin su Inna da Mumy to tabbas laifinsa yafi yawa, dan a matsayin sa na uba, miji abinda ya aikata shi kansa yayi alawadar dashi, tun ma daga auran mahaifiyar Jalila zuwa zaman da sukai...... Dady ya kalli Abba jiki a sanyaye yace "Ranka ya dade nace........" Abba ya kalleshi, Dady yanda yaga ya kalleshi ya daure yadanyi shiru...... ********** Hassan na shiga ya kalli kitchen, Ameera ce ta fito rike da kofi tana shan abu, tana ganinshi ta matso tace "Yaya." Kallanta yai yace "baki tafi islamiya ba?" Tace "ai yau alhamis." Yace "okay." Ya wuce sama, da sauri ta koma kitchen ta taba Jalila tace "Aunty mai sanyin ya dawo...." Jalila ta juyo ta taka kafarta, Ameera ta saki yar kara Jalila tace "bari na fadamai wai mai sanyi." Ameera tace "wayyo Allah na ki rufamun asiri." Jalila tana dariya ta fito, da sauri ta hau sama tana murmushi, ina yaje dazu? Tana shiga ta taraddashi yana cire kaya, da sauri ta juya baya tana cewa "yaya ashe ka dawo." Yana cire kayan amma kallanta yakeyi, yace "nemana kike?" Juyowa tai ta manta sam da abinda yakeyi tace " naga......." Ganin ya cire rigar tasa gaba daya tai sauri sake juyawa, murmushi yai yana kallanta, Jalila menene tsakaninki da Sageer? Me ya faru a baya? Anya ya dace nama Sageer haka? Tambayoyin da yakeji kamar ya yimata kenan, ta juyo ita kuka da sauri tace "Yaya kasan me?" Kallanta yai, ta kara kallan jikinsa da sauri ta sa hannu ta rufe fuskarta. Murmushi yai sannan yace "ki hadiye maganarku tunda kunyata kikeyi, in kuma so kike in matso to." Tace "ka matso ina?" Takowa yai yazo inda take, idanu ta bude da sauri, ya sa hannu ya lankayo cikinta yace " haka kikeso?" Idanu ta zaro tana kallansa tace "yaya wlh ni......." Shiru yai yanayin fuskarsa ne ya dan canza, murmushi yai sannan ya saketa yace "Mahaifinki fa yazo." Tace "yaushe?" Yace " yanzu ya shigo, da alama yazo ganin yar sa ne." Tace "hmm yadai zo abinda yazo yi, ko an turoshi." Hassan ya kalleta kamar zaiyi magana sai ya fasa, cikin toilet ya shiga ya rifo kofar. Da kallo ta bishi tare da yin ajiyar zuciya..... Itakam batasan ya akai take tsananin san ganinta da Hassan haka ba, lalai yanzu ta fahimci kaunarshi ta fara yin nisa a ranta. Dolene ta je gun Goggo ta fada mata dan itakam yanzu tanajin Hassan har ranta........... #OneLuv💕 [12/7, 10:12 PM] El-hajj: *_🗯JALILAH!!🗯_* Written By : *AYUSHER MUHD* ✔ote me on wattpad : *Ayusher Mohd* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* (_D home of expert and perfect writer's_💡) Day *59* Ummy tabi Sageer da kallo, yanda ya ajiye waya da sauri yamik'e bayan yagama ansa kiran da'aka masa, sama yahau da sauri, Hassan na kwance ya shiga bai ko jira ya amsa sallamarsa ba, yasan Jalila na kasa. Hassan na kwance yana tunanin abinda ke faruwa tsakanin Sageer da Jalila yaji shigowar mutum.
🏠