ukan da kikai ya bayyana min."
Kallansa tai da sauri, da gaske? Abinda zuciyarta ke tambayarta kenan......
***********
"Ya kukayi da mijin naki?".
Innace mai maganar tana tattara wasu takardu waje d'aya.
Momy tace, " ya amince inna, k'ilama zuwa gobe yaje ya dawo da ita".
"Humm, Ku azatonku zata dawo cikin sauk'i? kokuwa ita Jalilan kuna tunanin zata amince cikin sauri?".
"To amma inna kinsan da hakan miyasa kikace yaje d'in?".
"Kallonta inna tayi da k'yau, kafin tasaki guntun murmushi "Shi dai yaro yarone, aii sometimes bana banbance tunaninki dana Safeenah dama kisamin ido kiga inda na dosa, tunda ke kullum naki hasashen daban, ke ba komai a gabanki sai wannan mijin naki da ba abinda zai tsinana miki."
Tabe fuska Momy tayi, "to nidai Dan ALLAH koma miye dai kika shirya banason yataba mutuncin Abakar, dan nikam bazan dauka ba."
Sosai inna ta kalleta kafin tace, "bazai ta6aba, tashi kije 'yar gatan miji".
Kuma had'e fuska Momy tayi, kafin tatashi, tasan bak'ar maganace inna ta fad'a mata, itakam koma miza'ayi saidai ayi, bazata bari a wulak'anta mata mijiba ehe.
[12/7, 10:10 PM] El-hajj: *_🗯JALILAH!!🗯_*
Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
2pages
*58*
Alhamdulillah zuwa yanzu nutsuwa tazoma hassan, dan a kwanakin nan ko kad'an ciwonsa baya tashi.
Abba da Ummy sunma rasa wani irin farin ciki zasuyi, ga wata k'aunar jalilah dasukeji har cikin jininsu, yarinyar tazamarma zuri'arsu alkairi.
Ummy ta kalli Abbah dake zaune yana kallon labarai, fuskarta d'aukeda murmushi tace, "wlhy bansan wane irin alkairi zamu yima yarinyar nanba mu nuna mata jin dad'inmu akan sauyin rayuwa data kawo a duniyar Hassan".
Kallonta Abba yayi shima yana d'an murmushin, kafin ya maida kansa ga TV "gaskiyane, yarinyar ta cancanci kowanne irin alkairi, Dan ko'a mafarkina bantaba kawo zamu sami wani cigaba ba akan ciwon Hassan, dubi dai irin shekarun damuka d'auka muna famar bin likitoci na kasar nan da kuma na ketare, sosai nake jin dadi da alfahari da auran yarinyar nan."
"Ta cancanci a k'aunaceta kam....."
Maganar Ummy ta katse saboda jin wayarta na ringing .., daga ita har Abba wayar suka kalla, cikin damuwa Abba yace "ina ganin kawai acire layinnan, idan takira taji baya aiki ai dole ta hak'ura ko?"
"Ba cirewa nak'iba, muhimman mutane dake da number d'inne damuwa ta kuma kaga aii suna kira ai, amma kai yakakeji yanzu gameda ita? dan Allah zuciyarka kadai zaka duba karka damu dani ko su Hassan."
Shiru yai yana kallanta kafin yai mata murmushi ya kamo hannunta yace "Hummm....Alhmdulillah, dan kaso mafi yawa yaragu, yanzu sai lokaci-lokaci ma nake tunota, sabanin da danakejinta har raina, lalai ba shakka na tabbatar yanzu wani abun sukamin, sai dai Allah ya rabamu da sharrin mutane ni........
Ummy ta kalleshi tare dayin yar dariya kadan tace
"miye nak'in k'arasawar to?"
Shima Abba yar dariyar yayi "Ummyn Hassan, yanzu da Hassan zai yajini ai sai an samu wata yar karamar matsala, shi da bai had'a damuwar ummynsa data kowaba."
Ummy tai murmushi tace "Kaima kasan Hassan tun yana yaro haka yake, zan iya ajiye Husain nadan shiga ko toilet amma shi yana tsaye a kofa yana jirana, ko ina zani yana biye dani, sannan kaima kasan yanda Hassan ke tsananin kaunarka, na tabbatar abinda yake zargin ya aikata shine dalilin dayasa yake neman janyeka daga jikinsa saboda in kasani kar abin ya wahalar dakai."
Murmushi ya mata shima sannan ya saki hannunta yace "na sani, sannan ko da wasa ni ban dauki abinda yakemin a matsayin haka ba, tunda ni nasan yanda ya damu dani, tsautsayine dai da kaddarar data afka mai, Allah ne kadai yasan yaro dan shekara goma sha ya yai rayuwarsa a wannan dakin...."
Ummy tai shiru cikin tausayi tace "sai nakeji duk laifin nawa ne, kamar nice ban kula dasu yand......"
Kallan daya mata ne yasa tai shiru.......
Yace "mu ma wadanda suka rasu addu'a mu kuma mu nemi cikawa da imani."
Tace "hakane Allah ya jikansu da rahama, amma zaka fadawa mahaifin Sudais ne?"
Yace "su da basa kasar? Sai dai insun dawo mayi maganar."
Nan ta jinjina kai tare da kara maidakai kan Tv din da yake kallo.
*********
Bayan sun kammala had'a breakfast Ummy tabar Jalila ta karasa sauran dan dama haka suka saba, tana cikin shirya abincin a dinning Sageer ya fito, sotake yau Hassan yafito ayi breakfast d'in dashi, shiyyasa bata d'iba musuba, ta shirya komai a kan dining.
Tsayawa yai yana kallanta yana jin dadin yanda ta canza musu gida, dan da a koda yaushe matsalar Hassan sai ta maida gidan kamar ba kowa, amma yanzu kam Alhamdulila.
Ji tai ance Jalila!"
Juyowa tai ta kalleshi tace "Un.... Ya Sageer ina kwana?"
Murmushi yai sannan yace "Jalila mungode, mungode sosai da farincikin dakika kawoma family dinnan wannan shine abinda naso ki fahimta a waccan ranar, Yaya shine yafi cancanta da samun irinki, amma dan ALLAH ki gafarceni, da. nakula har yanzu k