auri tadan kurbi shayin tadan gutsiri bread kadan tadan ci, tana jin alamar tada mota ta suri jakarta da hijab dinta.
Goggo tace " kidan kara ci mana ai naga motar sai tayi zafi"
Jalila tace "Goggo ai yanzu ba late a rayuwata."
Tai waje da gudu a ranta tana cewa "ina san bari Uncle Ya ganni a cikin late comers?"
Ta riga su Safeena ma fitowa, a cikin mota ta sa safa sannan tadan karkade sandal dinta.
Safeena ta tabe baki tace "Jalila nikam dan Allah ki daina karkadomin disease."
Jalila ko kallanta batai ba ta kalli madubin gaban mota ta shiga dan duba fuskarta, Safeena ta kara jan tsaki tace "Mutum sai kace wanda zaije tallar kai, sai wani iyayi akemana, ni wlh na tsani iskancin banza."
Jalila ta kalleta tace "ke da wa?"
Tace " tambaya kike?"
Jalila ta tabe baki tace " ba tambaya nake ba dan na kula ke kullum cikin neman masifa kike."
Safeena ta bita da harara.
Fuskarta ta maida jikin window tana kallan titi tare da tunanin yau da wani ido zata kalli Sagir?
Ita duk kunya takeji.
Yana tsayawa ta sako daga motar sannan tama Yasmeen bye bye.
Tana kokarin shiga makaranta taga mota tayi parking a gaban makarantar.
Jalila ta juya tare da kallan motar, kamar tasan motar nan, kara kallan motar tai sannan ta juya tare da cewa "in ma na san motar meye nawa a ciki?"
Jitai ance Jalila!
Tsayawa tai dan ta gane muryar mai maganna.
Sagir yasa kanshi a cikin motar bayan ya fito, yace "Yaya godiya, zakaxo d'aukana?"
Kallansa Hassan yai sannan yamai alama da hannu akan ya cira kansa daga cikin motar.
Sagir ya fita tare da daga mai hannu, juyawa yai ya kalli kofar, gani yai bata gun.
Murmushi yai a ransa yace " naji dadin ganinki."
Shiga cikin makarantar yai fuskarsa dauke da fara'a.
Kasancewar yau friday karamar rana ce sannan Sagir shine last period dinsu.
Kafin ya shigo Jalila ta kalli Zarah tace "Zarah yau bakizo da sosan hoda bane?"
Zarah ta mata kallan mamaki sannan tai dariya tace "yau kece da kanki?"
Jalila ta dan canza fuska tace " in an tashi ba gida zani bane, ba kuma nasan inje fuskata na maiko."
Zarah tace "sai ki bari sai an tashi sai ki nema bawai tun yanzu ba."
Jalila tace "ana tashi nake san tafiya b........"
Gaisuwar dataji anayi ne yasa tasan Uncle ya shigo.
Harara ta makama Zarah sannan ta sunkuyar da kanta kasa.
Uncle kuwa ko kallan ida take baiyi ba har ya fara lesson dinshi.
Ganin baya kallanta ne yasa tadanji ba dadi a ranta sannan ta dago tare da kallan abinda yake koya musu.
Har ya gama sannan ta fita, yana fita Zarah fa miko mata sosan powder da madubi.
Jalila ta ture hannunta tace "banaso."
Sannan ta maida kanta kan desk ta kwanta, Zarah tace "tashi mu tafi."
Jalila tace " jeki ni sai anjima zan fita."
Zarah ta fita tai gaba, tana kwance har aka wa watse, idanu ma ta rufe kamar mai yin bacci, batasan sanda ya shigo class din ba.
Ya nemeta a waje bai ganta ba shiyasa yai tunanin ajin, kallanta ya tsaya yi yana murmushi, a hankali ta bude idanunta dan jin kamar ana kallanta.
Idanunta ne suka sauka akan fuskarsa shagwabe fuska tai dan ta tabbatar kila tunaninsa da takeyi ne yasa take ganin kamar shine.
Maida idanun tai zata rufe yace " fushi ake da ni ne?"
Da sauri ta bude idanunta tana kiftasu, sannan tai saurin komawa ta zauna, Sagir yace " me kike a class ke kadai?"
Batasan me ya sameta ba kawai ganintai ta wani hade rai wai ita a dole an mata laifi.
Sagir yace "Da alama wannan Malamin yayi laifi kenan?"
Kallansa tai fuska a hade tace " ba kai bane dazu ko kallan inda nake bakai ba?"
Tayi mamakin canzawar ta da kuma yanda take magana, a ranta tace "Lalai Jalila wato kin zama kwarariya."
FSagir samun kansa yai da darawa sannan yace " Nayi laifi, sai dai kin manta dazu Uncle Sagir ne malamin student a ajin?"
Tace "Yanzu fa?"
Yace "Yanzu kuwa Urs Sagir ne."
Da sauri ta sa hannu ta rufe fuskarta.
Kallanta ya sakeyi yace " ba haka bane?"
A hankali tace "Hakane."
Murmushin jin dadi yai sannan yace " tunda na ganki hankalina ya kwanta dan dama Abbana zan raka wani guri, nace bari nazo na ganki."
Kallansa tai tace "Okay, sai Monday kenan."
Yace "Kai! Har sai monday fa ko?"
Tace "ka manta yau friday?"
Fuska taga ya canza yace "gashi naga alama ke ko yar wayarnan baki dashi, anya zan iya jure missing dinki har sai monday?"
Kanta ta sunkuyar kasa tana murmushi, ajiyar zuciya yai sannan ya matso daf da ita yace "bari nai full charge yanda zan cancana battery dinA."
Kallansa tai sannan ta maida idanunta kasa tana murmushi.
Ido ya kura mata sosai sannan ya ce "Na tafi."
Sai dayaje kusa da kofa sannan tace "sai anjima."
Juyowa yai sannan ya juya ya tafi.
Ta window ta bishi da kallo, wani zazzafan so na ratsata.
Sam ta shagala da tunani kafin ta farga ta fito da sauri,
Tafi minti goma a tsaye taga dai ba alamar su Safeena, sannan ba alamar ma d'alibai suna wucewa, lalai ta tsaya soyayya antafi an barta, yau tana cikin wani hali dan tasan masifa kam b