ma yace, "A nan zaki kwana?".
Baki ta d'an turo gaba, ta yunk'ura zata tashi, amma saita kasa, saboda har yanzu yana rik'e da ita.
A shagwabe tace, "to taya zan tashi? bayan kamin d'aurin goro".
Firicin nata yasakashi sakin guntun murmushi, ya janye hannunsa batareda ya tanka ba.
Kanta kawai ta cire daga k'irjinsa, amma bata tashi a cinyarsa ba tace "Yaya wai ina kaje?""idan kin gama more cinyar itama saiki d'aga, idan kuma zaki biyane to?."
Baki takuma turowa, ta yunk'ura zata tashi tana k'unkuni
Harta mik'e yarik'o hannunta ya dawo da ita.
"Ah ah, mikuma nai?"
Hannunsa duk biyu yasaka ya zagayeta dasu, yakawo bakinsa kusada kunnenta.
"kina son sanine?".
Juyowa tayi ta kallesa da sauri, amma batace komaiba, saboda gabanta dake faduwa.
Ya huramata iskar bakinsa a fuska, yana kallon idonta dayay ja yak'ara d'an girma.
Yace "kin tabbatar ba saboda ki zauna kika sa turare a idan naki ba?"
Kallansa tai ta hade fuska tace "Yaya wai......."
Kauda kanta tayi, zuciyarta tana mamakinsa....
Barakai k'arshen tunanin taba taji yasaka hannun damarsa yadawo da fuskarta saitinshi.
Kafin tasamu damar magana taji bakinsa kan labanta.
Waro idanunta tayi saboda mamaki, shima ya waro nasa sosai kamar yanda tayi, sannan yahad'e bakin nasu sosai.
***********
Ummy kuwa koda tashiga d'aki sai ta tadda Abba zaune yana duba wasu takardu, shiru tayi nad'an wani lokaci tana nazarinsa, kafin tayi sallama. ya d'ago idanu yad'an kallrta ya amsa sallamar tata.
Suka d'anyi shiru zuwa 2minutes. Abba yakatse shirun da fad'in "Hassan fa?".
Sanyi Ummy taji aranta kafin tace, " yana lafiya. dama zan sanarma lokacin salla yayi".
Kansa ya jinjina mata, ya ajiye takardun hannunsa yamik'e zuwa bathroom. ita kuma zama tayi abakin gadon tana binsa da kallo, takasa tantance yanayin dayake ciki gaba d'aya. babu dad'ewa yafito, baiko kalleta ba yace, "naje masallaci".
"Adawo lafiya".
Ummy tafad'a tana mik'ewa tashiga toilet d'in domin d'auro alwala itama.
**********
Tunda suka dawo inna takasa zaune takasa tsaye, maganar family d'in Taura kawai take juyawa a zuciyarta, gakuma dadyn jalilah a gefe daya zame mata k'ayar kifi a mak'oshi, Tarawa wace hanya zatabi 'yarta ta fahimci manufarsa.
K'aramin tsaki taja, kafin ta zauna tareda d'aukar wayarta tana dannawa alamar akwai abinda take nema.
" humm" tafad'a tarefa ajiye wayar tana mik'ewa, sai kuma tace, " dukanku nasan hanyar dazanbi nai maganinku aii"
Ni dai nace, "humm".
************
Sun kai adadin wasu mintuna Hassan na baje kolinsa, kafin yacire bakinsa yana guntun murmushi.
Jalila kam kunya tasakata sinne kanta a jikinsa, sai kuma ta zame ta sauka daga cinyarsa takoma kan gado, bai ce komaiba shima yamik'e bayan yakai dubansa ga agogon dake d'akin.
Kallonta yad'anyi ya kauda kai, yanayinsa ne ya canza ya kalleta yace "Jalilah! Har yanzu Abba baice komai ba, kinganshi ne?
Shiru tayi tana kallonsa, shikuma yacigaba da tafiya.
Saida yakama k'ofar toilet d'insu zai bud'e sannan yajiyo muryarta tana cewa "amma Yaya kaimafa nakula matsoraci ne, a haka kamar....."
Kallan daya mata ne yasa tai dif tana sinne kai, fuska ya hade ya nuna kansa da d'an yatsa "ni ne matsoracin?"
Dariya tayi kawai, amma batace komaiba.
Ya jinjina kansa sannan ya ida bud'e k'ofar yana fad'in "lokaci zai nuna a gane wanene matsoraci tsakanin ni da ke yarinya"
Bataji miyaceba sosai, Dan acikin toilet ya k'arasa sauran maganar, babu dad'ewa yafito yana gyara hannun rigarsa alamar yayo alwala, itama alwalar ta tashi tai, dan dazu tai wanka, ita dama bata dadewa intana period.
Lokacin data fito shi harya fara salla, itama saita shinfid'a abin sallah abayansa ta fara tata.
Bayan sun idar ta kalleshi yana zaune inda yai sallar, yayi shiru alamar yatafi duniyar tunani, a wani halin Abbansa yake ciki?
Daurewa tai cikin k'arfin hali tace "Yaya nakawo abinci"
Kansa ya jinjina mata batareda ya kalleta ba ta mik'e tana cire hijjabin jikinta, kafin ta d'akko tiren ta dire a gabansa, yauma bayan tagama zuba masa, harta janyo wani plate d'in zata zubama kanta yarik'e hannun, daga ita harshi suka kalli junansu a tare, sai kuma yasaki ya ture plate d'in gefe, ya d'auki d'ayan spoon d'in yasaka a inda tazuba abincin.
Sai da yafara ci sannan itama tafara cin, babu mai magana acikinsu, har sukai rabin abincin.
Sai can jalilah tace, "Yaya mizai hana ka fara gwada shiga masallaci cikin mutane yin jam'i?"
Ido yad'ago yad'an kalleta, baice komaiba har suka kammala, har ta d'auka bazai ce komai ba. tana tattare kwanikan taji yace "Kina tunanin zan iya?"
Kallansa tai jiki a sanyaye, yace "a koda yaushe inaga taron mutane sai naga kamar lokacin da mutane suka taru akan su Husain."
Shiru tai kafin tace "banyi tunanin hakan ba n......"
Yai saurin cewa "I won't stay like this forever, nagode da shawararki sallah cikin mutane tafi lada."
Kallansa tai cikin jin dadi tace "tam Yaya."
"Humm" ya fad'a yana mik'ewa, kayan jikinsa yafara k'ok'arin cirewa, dan haka Jalila tayi saurin d'aukar tiren tafice.
Binta yayi da