fice.
****
Su Ummy nazaune haryanzu a parlor itada Sageer, bai kalli inda sukeba yafice da sauri, dan kunyar had'a ido yakeyi da Ummy.
Da sauri Ummy ta yunk'ura zata bishi amma Sageer ya rik'e hannunta da sauri, juyowa tayi ta kalli sageer d'in, idonta harya fara tara kwallah, Sageer ya girgiza mata kansa,
"A'a Ummy kibarshi"
Ummy ta kalli hanyar daya fita tace "Yaza kace Na barshi Sageer? bakaga a yanayin daya fita bane?".
Sageer ya kalleta yace "Nagani Ummy hakan ne ma yasa nace ki barshi, addu'a kawai zamu mai."
Shiru Ummy tayi takasa magana.
Fad'uwar Abu dasuka jiyo a kitchen ya sakasu juyawa su duka suna kallon kofar kitchen d'in, sai kuma suka tafi kitchen d'in a tare.
Shigowar su tasaka jalilah dake tsuggune tana kwashe fasashshen kofin daya silmiyo daga hannunta wanda ya fashe haryasa su Ummy sukajiyo yasata d'ogowa tana kallonsu.
Da sauri Ummy ta k'araso gareta tana fad'in "bakiji ciwoba ko jalilah!?".
Kai jalilah ta girgiza mata alamar a'a sannan tace
" a'a Ummy, banji ciwoba".
Ganin haka sai Sageer yajuya yafita.
Jalila tad'an bishi da kallo, kafin tadawo da kallonta kan Ummy dake mata magana.
"Jalilah mijinki fa?".
K'asa tayi da kanta cikin kunya tace " Ummy yana d'aki".
"Baya d'aki gaskiya, dan yanzu yafita nama zata kema kina d'akin aii? Sam ban kula da saukowarki ba."
Cikin d'an zaro ido waje na alamun tsorata Jalilah tace, "Ummy yanzufa nafito, nabarshi a d'akin a kwance, naga kuna magana ne da ya Sageer, shiyyasa na taho nan banyi magana ba".
K'aramar ajiyar zuciya Ummy ta sauke, sannan tace,
"Amma a wanne hali kika barshi? Ni na kasa ganewa."
Jingina sosai Jalila tad'an karayi da fridge din dake bayanta, tareda murza tafin hannunta na dama.
"Ummy ki kwantar da hankalinki, babu wata damuwa wallahi, wannan fitarma k'ilan akwai zaman cikin ne ya isheshi".
Ajiyar zuciya mai k'arfi Ummy ta sauke, sannan tak'arasa inda Jalila take tsaye, hannunta datake murzawa ta kamo, dan zatonta ko Jalila taji ciwone da kofin data fasa".
"Ummy babu komai fa, ba ciwo najiba".
Murmushi Ummy tayi, "ai nazata ciwone kike boyemin, bara nataya ki mu k'arasa girkin".
Da sauri tace "Ummy kibarshi na k'arasa dan Allah kije kawai ki huta".
"A'a, muk'arasa kawai, kafin mijinki yadawo".Shiru jalilah tayi saboda kunya, a tsanake suka gama komai, Ummu dai tausayin Hassan duk ya dameta, sai da taga sun kusa gamawa sannan tafito Jalila ta k'arasa.
Babu kowa a falon, Sageer ma ya shige d'akinsa. Ganin haka sai Ummy tanufi wajen Abbah, dan duba halin dayake ciki.
Bayan jalilah ta kammala komai ta d'auki abincin su ta haye sama.
Ajiye tiren tayi, sannan ta d'an gyara gadon dasuka bata d'azun, gefen zuciyarta na tunanin ina Yaya yaje? itadai tasan lafiya lau tafita tabarsa, to miya fasu ne?.
Haka taita 'yan tunane tunanenta harta kammala, tashiga toilet tayo wanka, a gaggauce tafito ta shirya, dan batason Yaya yashigo ya ganta ba kaya kamar rannan.
Babu maganar kwalliya a tsarin jalilah, tasaka doguwar riga ta material, d'as takama jikinta, ta d'aura d'an kwalinta simple, harta bar jikin mirror sai kuma tadawo, ta d'auki turare tana fesawa, abisa tsautsayi kuwa ta fesowa fuskarta, sai cikin idonta Na haggu.
Karamar kara tasaki, tareda saurin rufe idon da hannu daya, dayan hannun kuma tana yarfawa tare da kiran "wayyo Goggona".
A haka Hassan yashigo dakin ya sameta.
Kallo yabita dashi, ganin yadda take tsalle-tsalle taki tsayawa waje daya saita bashi dariya, amma bai yiba ya zauna bakin gadon tareda ajiye key da wayarsa agefe.
Jalilah batasan dashiba, dan kokad'an bataji shigowar saba, sai tsalle-tsallen ta takeyi tana shiiiiii da baki, har yanzu hannunta dafe da idon, d'ayan kuma tana yayyarfashi, lokaci-lokaci takance "wayyo Gwaggona, Goggo kizo na makance".
Tausayi tafara bashi, yabita da kallo daga sama har k'asa, sai yanzu yalura da gwangwanin turaren dake k'asa a yashe, da alama shine tasama idonta.
Da sauri ya mike ya matso kusa da ita, sannan yakai hannu yariko hannunta datake yayyarfawa.
Tsorata tayi, tace, " Wayyo Allah na, wanene?".
Bai bata amsaba, suka je kusa da gado ya zauna, jawota yayi ta fad'o jikinsa saman cinyarsa.
Jiyayi wani mugun shock ya shigesa, har sai da yad'an rintse idonsa. Itakam jalilah k'amshin turarensa yasa tagane shine, dan haka saita nutsu, tabar mutsu-mutsun datakeyi.
Hannunta data rufe idon yajanye, ya kwanto da kanta saman k'irjinsa, yasaka hannunsa d'aya ya bud'e idon da k'yau, d'ayan kuma ya tallafo kanta sosai, sannan yafara hure mata a hankali, idon yayi jawur kuwa.
Yanda yake matanne yasakata yin luf ajikin sa, gakuma k'amshin turarensa mai dadi tana shaka.
Ya dad'e yana hura mata idon, sai da ya tabbatar ya huce sannan ya daina hurawar, amma yaki sakinta.
Bud'e idon tayi ahankali ta saukesu akansa, ganin ita yake kallo saita d'anyi k'asa da idanunta, a hankali ta furta "Na gode yaya".
" Uhhm".
Kawai yace mata, sai kuma ya k'ara hura mata iska a fuska.
Ta bud'e idon sosai tana kallonsa.
Da ido ya nuna kanta dake kwance a k'irjinsa, sai ku