me zan nemi hucewa akan fridge? Laifi akamin?"
Tace "ina na sani?"
Juyawa yai ya fita yana cewa "ke dai da kike tsoro sai ki karashi zama a ciki."
Tana neman magana ya fita, haushi ne ya kamata ta kashe gas din ta biyoshi.
Yana shiga falon itama tana shiga, da Sageer suka fara hada ido, tai saurin daukewa sannan ta karaso.
Hassan na zama yaga shigowarta, murmushi yai a ransa ta shiga ta zauna a kasa daga gefe, ta gaida Inna da Mumy.
Inna cikin sanyin murya tace "Jalila ki yafemana abinda muka aikata miki."
Mumy ma tace "kiyi hakuri Jalila, bamu kyauta ba."
Kallan Hassan tadan yi taga ko kallanta ma bayayi tace " ya wuce."
Kallanta yai, itama ta kalleshi, ta maida kanta kasa, ganin zaman nasu ba so ake ba yasa sukaitama Jalila dasu Abba godiya, dan Abba yace zaibar kudin zuwa wani lokaci.
Haka suka fito suka shiga motarsu suka tafiAbba na shirin barin falon Hassan yace "Abba!"
Abba ya kalleshi yace "Hassan da magana ne?"
Hassan ya daga kai yace "dukanku, magana zamuyi."
Ummy cikin mamaki ta kalleshi, shima Abba kallansa yai.
Jalila ta juya zata fita, da sauri yace "Jalilah."
Cak ta tsaya saboda yanda ya kira sunanta, ya kata alama data dawo falon.
Komowa tai ta zauna, bayaji zai iya jawabin nan ba tare datana kusa ba.
Falon yadanyi shiru, Sageer na zaune shima, Hassan ya fara da cewa "Abba kayi hakuri ka yafemin, duk wani hukunci da zakamin zan dauka ko menene shi kuwa, sai dai ina neman yafiyarka a gareni."
Jikin Abba ne yai sanyi yace "rabuwa kakesanyi da matarka?"
Hassan ya kalleshi yace "Abba Husain...."
Ummy ce ta kalleshi da sauri tace "Hassan."
Kallan Ummy yai ya saki wani sansanyan murmushi yace "Ummy nine sanadiyar mutuwarsu."
Ummy da Abba a tare sukace bangane ba???
Jalila kam Hassan kawai take kallo sai idanunta da suka ciciko da kwalla.......
Hassan yace " a ranar sunan Ameera............"
Nan ya kwashe komai ya sanar dasu, gaba daya falon hankalinsu ya tashi najin abinda ke faruwa, sai dai Hassan nakaiwa karshe bai jira amsar wani daga cikinsu ba ya tashi da sauri ya hau sama, Ummy na kiransa ko juyowa baiyi ba.
Jalila ta mike da sauri tahau sama, yana shiga itama ta shiga.
A bakin gado ta ganshi yana neman zama, hannunsa ta riko da sauri tace "Yaya"
Da sauri ya jawota jikinsa ya rungume tsam, zuciyarsa na wani irin bugawa, yanda ya kankameta ne yasa tai shiru, cikin wata irin murya yace "Wani hali Abba zai shiga? Yaji dansa ne yai sanadiyar......"
Kasa karasawa yai saboda raunin da zuciyarsa ke neman yi, Jalila tace "Yaya wanda bai sanka ba inya ganka zaiyi tunanin zuciyarka rike take gam, ba tausayi a cikinta, sai dai wanda ya zauna dakai a hankali zai fahimci zuciyarka cike take fam da tausayi."
Yace "ke tausayi hakan yai miki kama?"
Tace "sosai zuciyarka saboda tsananin tausayinta ne yasa take zargin kanta da aikata laifin da ba ita ta aikata ba."
Hassan yace "ya isa haka nan Jalila, na san kina fadar hakan ne dan hankalina ya kwanta, please keep quiet."
Shiru tai sai dai haryanzu bai saketa ba, Sageer wanda hankalinsa ya tashi ya taso da sauri ya gansu a haka a cikin dakin, juyowa yai jiki a sanyaye fuskarsa na dauke da murmushi a ransa.
Yana saukowa Ummy tace "Sageer ina Hassan din?"
Yasan yanda Ummy ke tsananin san Hassan, yace "karki damu Ummy matarsa na gunsa."
Komawa tai ta zauna ta kalleshi, yace "Abba fa?"
Tace "ya shiga daki."
Sageer ya zauna a kusa da ita yace "Ummy kinsani ko kema sai yanzu?"
Ta share kwallarta tace "bantaba sani ba, Sageer Hassan haka yai shekara sama da 15 cikin zargin kansa?"
Sageer cikin tausayawa yace " Ummy ni nama rasa me zance."
Shiru sukai suma........
Hassan kam ya dade manne da ita kafin daga baya ya saketa, kallanta yai sannan yace "na matseki ko?"
Tai murmushi tace " to ni yanzu yaya wace amsa kakeso na baka?"
Zama yai a kan gado sai kuma ya kwanta baice komai ba, harta juya zata sauka saboda girkin da ta kashe taji yace " Jalilah!"
Juyowa tai ta kalleshi sai dai sanyin jiki yasa ta kasa amsawa, yace " kina tunanin hankalin Abba zai kwanta?"
Tace "shima Abba zai fahimci ba laifinka bane ba."
Yace "nagode."
Kallansa tai sannan ta fito.
********
Dady ne ya kalli Mumy yace "ya kukai?"
Tace "ni wlh gaba daya na kasa fahimtar takamaimai abinda ya faru a gidan."
Dady haushi ya kamashi, amma ya murmusa yace " amma kina tunanin sunji haushina?"
Tace " ai dukanmu ma ko kamanta Goggo na gunsu? Na tabbatar sunsan komai."
Dady yai dan tsaki a ransa yace dolene ya je ya lalaba Jalila ai dama ba mai shiga tsakanin jini? Yana zuwa zaisan yanda zaiyi ta yafemai......
#OneLuv💕
[12/7, 9:55 PM] El-hajj: *_🗯JALILAH!!🗯_*
Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*Gaisuwa gareki BillynAbdul akoda yaushe ina miki fatan alkairi arayuwarki......*
*56*
Damuwa da rashin sukuni suka saka hassan gaba, gakuma jalilah tafice tabarsa shikad'ai a d'akin, jiki a sanyaye yasakko daga gadon, yad'auki wayarsa da key ya