nshi ya fahimci wannan bai bada ma'ana ba, kafin yai magana Sageer yace "matar gidansu babanta ce da yarta."
Cikin rashin fahimta yace "bangane hausar ba."
Sageer zai sake magana Hassan ya kalleshi, bai san sanda ya sa dariya ba yace "Tab amma lalai Sageer matar gidansu babanta?"
Mamaki ne ya kama Sageer yaya ne anya kuwa?
Hassan ya fahimci yanayin da Sageer ya shiga sai ya dan hade rai kadan ya matso kusa dashi kafadarsa ya dafa, yace "Me kake tunani?"
Sageer yai murmushi yace "kawai ina mamaki ne, banaji tunda nake na taba ganin kana dariya haka ba."
Yace "ni kaina na dade banyi dariya haka ba, kai ne yanda kai maganar ne banma san sanda dariya ta zomin ba."
Sageer ya kura mai ido cikin jin dadi, yana hamdala aransa.
Hassan ya juyarmai da kansa gefe yace " muje."
Murmushi Sageer yai sannan suka fito, tare suka sauko.
Ummy tana zaune a falo ta hangosu, tunda suka taho ta zuba musu ido cikin jin dadin ganinsu tare, karasowa sukai Hassan ya hade fuska gam, ya zauna daga kusa da Ummy.
Sai daya gaishe da Abba ya gaisheta sannan ya kallesu ya gaishesu a wani irin yanayi da inhar kana gurin sai ka dara.
Sageer ya juya kai yana guntse dariyarsa, Inna ta amsa cikin fara'a tace " sannu Malam Hassan, ina Jalilan tamu?"
Bai amsa mata ba yace "Abba ance inzo nayi baki."
Abba yace "bakin a sunan naka ne amma gun matarka sukazo."
Hassan ya juya bai ganta ba, Ummy tamai alama da tana kitchen, kallansu yai yace "ayya, wani abun ne ya faru?"
Inna ganin yanda yai magana yasa hankalinta yadan kwanta tace "Hassan nasan zakuyi tunanin cutarku mukai muka yaudareku sai dai maganar gaskiya ba haka bane, duk laifin nan nawa ne, ganin yanda Taura ya taimakemu ne yasa nai zauna nai tunani, Safeena bata dace da sirikar Taura ba, yarinyace mai san jikinta, gashi bata iya ko girki ba, ni kuma ina tun.........."
Hassan ne ya katseta yace "Tambaya nai kawai wani abun ne?"
Inna ta kalleshi, Mumy tai murmushi tace "ba wani abun bane, ita Inna tana tunanin bata kyauta ba gun yaudarar da muka muku shine mukazo neman yafiya, da neman taimako akan karku kwace kudinku."
Hassan ya kalli Abba yace " kudi na Abba ne ra'ayinsa ne ya kwace ko ya barku, ita kuma Jalila da mahaifiyarta da kukama laifi su zaku nemi yafiya agunsu ba mu ba, sannan na tabbatar wannan neman yafiyar bawai anzo yinshi bane saboda zuciya ta saduda anzo ne saboda ana san duniya."
Ya kalli Abba bai jira amsarsu ba yace "Kafin su nemi yafiya a gunka ina tunanin me zai hana a kudinmu na company dinsu mu sai share dashi? Kaga muma ya zamana munada iko akan su, saboda ni gaba daya mutanen nan basumin ba."
Ummy ce tai saurin tabashi, ya kalli su Inna ya kalli Mumy sannan ya kalli Abba yace " duk wani tunani da kukeyi akan mutanen nan sun wuce nan, ku duba abinda sukama Goggo da Jalila."Inna tace "munsani abinda muka aikata bai dace ba."
Hassan yace " Ina shi mutumin yake?"
Mumy tace "mutumin wa kenan?"
Sageer yace "mahaifinta? Bashine ya dace ya fara zuwa ba?"
Mumy tai saurin cewa "yayi tafiya ne."
Hassan yace " ohhh!"
Inna ta kasa dakai tace "na sani mu masu laifine agareku sosai, sai dai ya zamuyi? Shi mahaifinta bai taba nuna ya damu da ita ba, bai taba nuna mana damuwarsa akan matar data haifeta ba, sai dai yana neman yanzu na sakar mai ma company din, to ni ina tunanin kudinka dake ciki......."
Abba yai shiru yana kallan Inna wato a wayau tana nunamai ba fa sune masu laifi ba tsohon tane, ai in suka fahimci hakan sa dau mataki akanshi.
Sageer ya kalli Abba yace "dama ai duk mai laifin mahaifinta ne."
Abba yai shiru yana kallanta, tana ci gaba da bayani, akan yanda Dady ya banzatar da Jalila da Goggo.
Hassan kam mikewa yai ya bar falon.
Me Ummy zata gani? Gani tai ya nufi kitchen mamaki ne ya kamata sai dai wani farinciki ne ya shiga ratsata.
Cikin kitchen din ya shiga, tana vegetables a tukunya ya shiga.
A bakin kofa ya tsaya yana kallanta, juyawa kawai take amma hankalinta na falo, jin alamun mutum yasa ta kalli bakin kofa.
Hassan na ganin ta juyo ya shigo kitchen din da sauri kamar ma wai baisan tana ciki ba.
Kallansa tai da sauri ta matso cikin zumudi tace "yaya ya kukai? Sun tafi?"
Yace "ke meya hanaki zuwa?"
Tace "kawai, banasan ganinsu."
Yace "kin tabbatar ba tsoro ne ya hanaki ba?"
Tace "ba wani tsoro ni kawai........"
Kai ya shiga jijigawa wai alamar ya fahimta irin na wulakancin nan.
Tadan kalleshi fuskarta a hade tace "kaifa? Abu ka shigo yi?"
Ya kalleta yace "me? Kina tunanin gunki nazo?"
Tace "bance ba." Tai maganar cikin sanyin jiki.
Yace "ah to gwara dai ki fuskanci reality."
Baki ta dan turo ta juya ta cigaba da suya, Hassan ya kalleta hankalinsa ya kwanta ya dauka ganinsu ya sata cikin wani hali.
Fridge ya bude yadan sha ruwa kadan dan karta gane, yanayi yana kallanta amma yaga ko kallansa bata sakeyi ba.
Da karfi ya buga murfin fridge din, juyota tai ta kalleshi.
Yace "wani irin fridge ne wannan? Daga sakeshi sai ya tafi?"
Tace "anya kuwa ba kai ka buga shi ba, naga ne baya haka."
Hassan ya kalleta yace " akan