n yanzu bafa kanka na hau ba."
Kansa ya juyar gefe yace "ni? Kin tabbatar bake kika fara ba?"
Ta saki baki tace "yaya tanan ka bulo? Su biyu fa kenan kana min haka."
Murmushi ya sake yi.
Da sauri tace "yaya kayi murmushi wlh."
Shiru yai yana kallanta sai dai yanayin fuskarsa ya canza yace "Jalila!"
Gyara zama tai a hankali tace "naam."
Yace "nagode."
Kallansa tai cikin mamaki, yace "zan sanar ma Abba komai, ko tsanata zaiyi ko hukuntani zaiyi zan dau komai, nagode da kika budemin zuciyata kika nunamin rayuwar daya kamata nai."
Kallan rashin fahimta tamai tace "ni?"
Yace "kin tabbatar zaki jure ganina a kasa?"
Tace "kamar ya?"
Yace "duk girman gadon nan sai na sauka?"
Tace "tare zamu kwana?"
Yace "ba haka kikeso ba dama?"
Tace "yaushe nace?"
Yai ajiyar zuciya yace "yanzu abinda na gani kenan kin fada a fuskarku."
Tai tagumi tace "oh ni."
Kwanciya yai ya dau littafinsa yace "ba abinda zan miki in ma shi kike tunani, tunda dai har kikai fitsara a gidan goggo ai kwana tare ba zai zama issue ba."
Jalila tai dariya tace "wallahi yaya na fahimci kawai so kake kai ta zolaya ta."
Bai amsa mata ba ya fara karatu, kwanciya tai daga can karshe tace "wai yaya mai kake karantawa haka kullum?"
Yace "kawai karantawa nake nai ta tisawa ina san dauke tunani daga raina."
Shiru tai tana kallansa, yace "inkingama kallan nawa sai kiyi bacci."
Da sauri ta rufe idanunta a haka har bacci ya dauketa.
Bargo ya ware ya luluba mata sannan ya kura mata ido yana kallo, Jalila! Jalila! Nagode da amincewa da kikai dani.
Murmushi ne ya sake bayyana a fuskarsa, sannan yai shiru yana tunanin Abba da Ummy dasu Sageer, gobe zai sanar dasu komai ya kuma nemi yafiyarsu, kome zasumai gani yake zai dauka tunda tana tare dashi.
Sai can ya kwanta yai bacci, bacci mai dadi yai wanda shikansa bai sani ba,bai farka ba sai biyar saura, wanda raban dayai irin baccin nan ya dade, addu'oi yai tayi da neman yafiya har gari yai haske kafin ya dawo ya kwanta, yaso tashinta tayi karatu amma yabarya saboda ganin yanda take bacci.
*********
Wajen karfe 9 suna aiki da Ummy a kitchen akai sallama, Sageer dake kallo a falo ya bude kofar, mamaki ne ya kamashi ganin Inna da Mumy.
Inna tace "Taura harya fita?"
Ya daure ya gaisheta kafin yace "yana nan."
Tace "ko zaka sanar dashi?"
Muryar Ummy yaji tace "Sageer wanene?"
Sageer yace " Matar gidansu baban Jalila ce."
Ummy tace "matar me?"
Yana kallansu yace "kishiyar Goggo."
Ummy tace oh Sageer akwai tsiya, kallan Jalila tai wacce tai tsuru tsuru, Ummy ta dafata tace "kin manta a inda kike ne?"
Kallan Ummy tai sannan tai murmushi tare da girgiza kai.
Ummy tace "shigo dasu mana." Sannan ta wanke hannu ta fito, a falo suka zauna.
Ummy ta karaso suka gaisa duk jikinsu a sanyaye.
Inna ta daure tace "Hajiya dan Allah a mana magana da Taura."
Ummy ta kalli Sageer tace "Sageer kira Abbanka."
Mikewa yai ya nufi falonsa.
Aiki yakeyi sanda ya shiga nan ya sanar dashi, Abba yace yana zuwa.
Jalila kam aikinta ta cigaba, tanaji harsanda Abba ya shigo.
Inna ta gaidashi kamar irin itace karama, Mumy ma ta gaisheshi.
Zama yai yace "lafiya? Da safen nan?"
Inna ta murmusa tace "dama munzo ne muyi bayani."
Yace "bayani?"
Tace "munsan kunsan komai akan abinda muka aikata."
Yace "sai akai yaya?"
Tace "laifinane, sai dai ina baka hakuri, muci darajar marigayi karka kwace kudinka."
Abba ya kalleta kamar zaiyi magana sai yace "Sageer yima yayanka magana."
Inna najin haka gabanta ya fadi, ita kanta Mumy hankalinta ya tashi tace "ai ba sai yazo ba, hakuri mukazo badawa."
Abba yace "na sani kuma na fahimta, matarsa ce wacce kuka wahalar kuka nemi tozartawa, hakkinsane ya yafe muku ko yaki, sannan ita yarinyar ita zaku ba hakuri ba ni ba, idan har yarinyar da mijinta sun yafe muku banaji ni inada matsala."
A ran Inna tace nasan Jalila batada matsala, babbar matsalar yaran nan......
***********
Kallansa tai tace "me kake nufi RAM?
Yace "haba Safeena ke sai yaushe ne zaki bar gidadanci? Baki kula duk mutane ba wanda yakesan harka dake ba saboda kauyancin da kike nunawa?"
Shiru tai tana kallansa kafin tace "To ya kakeso nayi wai?"
Yace "ki tashi dalla ki canza wannan shirmen na jikinki kisa wando da riga ki bar ragowar a hannuna, ni zan maidake fitaciya a skul din nan."
Kallansa tai cikin gamsuwa sannan ta kike........
#OneLuv๐
[12/7, 9:55 PM] El-hajj: ๐ฏ *JALILAH* ๐ฏ
Written By : *AYUSHER MUHD*
โ๏ธote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_๐ก)
*55*
Sageer ne yamai knocking, yana zaune a kasan carpet yayi shiru yana nazarin dayake damunsa.
Mikewa yai da sauri yace "shigo mana."
Sageer ne ya shigo ya kalleshi yace "yaya ashe ka tashi?"
Yace "na tashi tun dazu, inzo ne?"
Mamaki ne ya kama Sageer ya girgiza kai yana murmushi yace "baki kayi."
Cikin alamar mamaki yace "baki?"
Yace "eh daga gidan su Jalila."
Da sauri yace "Goggo ce?" A ransa yana fatan badai ta gansu ba? Da sauri yace inta ganmu sai tazo? Shika