kasa ne? Naga ka dade lafiya."
Kallanta yai sannan ya girgiza mata kai yace "ko daya."
Ta kalleshi bayan ya mike daga gun tace "Yaya nikam dan Allah meke damunka? Mafarki kakeyi? Ko.......?"
Sai kuma tai shiru, yace "ko aljanu gareni?"
Da sauri tace "ba haka nake nufi na...."
Ruwa ya dauko yasa sannan ya dawo ya kwanta, kallanta yai da take dukushe a gun yace "Hajiya zan kwanta."
Tace "Hajiya? Lalai Yaya matar da bata taba zuwa hajj ba, batama iya karatu sosai ba itace Hajiya."
Juyowa yai ya kalleta sosai yace "daki shiga islamiyya ku dinga zuwa da Ameera da kuma ki zauna a gida wanne yafi?"
Tace "in zauna a gida kamar ya?"
Tai tambayar tana kallansa, juyawa yai baice komai ba.
Da sauri ta kalleshi tace "da ka koyamin a gida?"
Idanunsa ya rufe da sauri tare da harde hannayensa, ta sako kanta tace "Yaya dagaske?"
Bude idanunsa yai, sam baiyi tunanin ganinta daf dashi haka ba, idanunsa ne ya sauka a nata, da sauri ta mike tsaye ta hau kan gado ta kwanta tare da saurin kashe fitilar dake jikin gadon.Kwanciya tai tana dan ajiyar zuciya a hankali.
Dakin ne ya baibaye da duhu.
Tana kwance sai dan juye takeyi, can tace "yaya kayi bacci?"
Shiru yai baice komai ba sai dai yana jinta, tadan sake ajiyar zuciya kadan.
Muryarsa taji yace "baki taba tambayata dan uwana ba, bayan duk wanda yaji sunana Hassan ya tabbatar inada Husain."
Juyowa tai ta kwanta akan tafukan hannayenta ta jiyo ta saitinshi, duk da duhu ya sa bata ganinshi tace "taya zan tambayeka abinda ka kasa fadama kowa?"
Shiru yai dan harta dauka bazaice komai ba sai taji yace " shekararsa 10 kenan da rasuwa."
Zatai magana taji yace "tare suka rasu da dan kanin Abba, Sudais wanda yazo gidannan karatu."
Jalila yanzuma hartace "sh........"
Ya kara katseta yace "karkice komai kijini kawai."
Shiru tai tana kallangun da yake.
Yace " karki kunna fitila."
Tai shiru, tare da kallansa, Hassan yana kwance yace "they died because of me......"
Ya fada tare da runtse idanunsa da karfi yana jin wani abu na tokare mai zuciya.
Wasu zafaffan hawaye ne suka zubomai, yace "He is a bright person, mutum ne mai tsananin hakuri, a koda yaushe cikin fara'a yake Jalila..........."
Nauyin da zuciyarsa taci gaba dayi, ga numfashinsa na seizing ne yasa yai shiru, saukowa tai da sauri har tana buge kafa ta matso kusa dashi.
Tace "yaya!"
Ta dauka abin ne ya tashi.
Jinta a kusa dashi ne yasa yasa hannunsa dan jin a inda take, a durkushe a kusa dashi ya jita.
Hannunta ya riko sannan ya kwantar da kansa akan kafafunta dake a durkushe.
Da sauri ta kalleshi.
Hannunta ya riko.
Kallansa tai zuciyarta na bugawa da sauri, a hankali tace "karka cigaba yaya inhar zuciyarka bazata iya dauka ba, sannan bansan menene yafaru tsakaninku ba amma na tabbatar ba............"
Yanzu ma katseta ya sakeyi, yace "don't comfort me."
Shiru tai, yace " nikaina bansan meyasa nakesan fadamiki abinda ban fadama kowa a duniya ba, sai dai ina alakanta hakan da zaman da nai dake sannan da yanda nasan komai naki."
A hankali ya lumshe ido zuciyarsa na kunna, yace "later....."
Kai ta daga tace " later Yaya.... sanda kaji zaka iya."
Kansa ya kara gyarawa, shiru tai sai jikinta dayai sanyi, zuciyarta na bugawa da sauri.
Ya dade a haka kusan minti ashirin kafin yaji an fara kiraye kirayen sallah, ita ta dauka ma bacci ne ya daukeshi, ga kafarta ta fara zafi.
A hankali ya dagata sannan ya mike ya kunna wutar dakin.
Haske ne ya baibaiye dakin, kallan juna sukai, ya dauke kai ya shiga toilet.
Yana shiga ya kalli kansa a madubi, yanzu kam ya tabbatar ya fara san yarinyar nan, garin yaya? How can i??? Ya furzar da wata iska.
A inda ya barta anan ya ganta, ya kalleta yace "me kike anan?"
Da sauri ta mike ta fara ninke bargo tace "bakomai."
Kallan fuskarsa tai, tanaso taga canji a tattare dashi, kallanta yai yace "kallan fa namenene?"
Ta mike rike da bargo tace "bakomai, ba kai na kalla ba."
Yace "then?"
"Uhmm yauwa toilet na kalla."
Sallaya ya shimfida batare da ya kalleta ba, ta mike da sauri ta shiga toilet.
Tana rufe kofar tai ajiyar zuciya tace "meke damun yaya? Ya tone din maganarsa ta koma ta da?"
Shima tana shiga toilet ya kalli kofar toilet din sannan yai ajiyar zuciya shima, ya tadda sallah.
[12/7, 9:54 PM] El-hajj: *JALILAH* ๐ฏ
Written By : *AYUSHER MUHD*
โ๏ธote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_๐ก)
*51*
Kallanta yai yace "bazaki shiga ba?"
Juyawa tai ta shiga dakin, ta ajiye tiren sannan ta kalleshi tace "Yaya abinci."
Bai kalleta ba yace "sai nayi wanka."
Ya fada tare da nufa ciki,, da kallo ta bishi tana mamakin halayensa.
Harta bude zata zuba sai kuma ta maida murfin kular ta rufe.
Hannu tasa ta janyo littafin da yake karantawa ta dauko, ta bude cikin littafin.
Ajiye littafintai sannan ta kalli hanyar toilet, ta mike ta fito falo.
Tv ta kunna tai shiru tana tunanin abinda ya faru tsakaninsu a daren jiya.
Kalamansa na kara dawo mata, meya faru a can baya? Wanda yake hanashi bacci?