a makaro dan kana tafin hannuna wlh.
(Nace damuwarki😏)
#OneLuv💕
[12/7, 9:53 PM] El-hajj: *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
✔️ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*49*
Goggo tana zaune tana kara bin gidan da kallo, hawayenta yaki tsayawa, ashe alheri ne a dukulle a tattare da sharrin da aka jefesu dashi.
Ba wani katon gida bane, falo daya ne babba sai 2bedrooms a cikin falon da toilet daya.
Sai tsakar gida kato wanda za'a iya ajiye motoci kananan guda biyu.
Ameera da Lantana dake sa labule ta kalla tama rasa ta ina zata fara, ashe a rayuwa akwai rana irin wannan? Shiyasa mutane ke cewa Allah yasa muci darajar 'ya'yan mu, a da bata fahimtar abinda ake nufi da hakan amma yanzu ta gane dalilin fadan hakan, in kai a rayuwa bakai sa'ar abokin zama ko iyaye ba sai ka nemi sa'a akan 'ya'yanka.
Hawayenta ta share, ko mahaifiyarta da mahaifinta nada rai?
Haka su kai ta aiki, itama tana tayasu, sai yamma su Ummy suka dawo, sun siyo abin kitchen, tv set, toilet, abinci da sauransu, dama zuwan farko aka siyo kujeru, gado da labulaye.
Haka suka taho musu da gashashiyar hanta da juice suka ci suka sha, Ummy ta nunama Goggo kawai komai ta samu tayi. Hamdalla bawai taita kuka ba, hakan yasa ta saki jiki sukaci abinci tanata godiya.
Sai wajen Magrib suka kammala komai, Ummy tace su tafi, sai asa ranar tarewarta.
Goggo tai shiru tana tunani, Ummy ta matso tace "lafiya? Ko kina tunanin zama ne gaba daya?"
Goggo tace " indai hakan zai samu nafisan hakan, dan maganar gaskiya kunyar gidan nakeyi.
Ummy tace "shikenan ai ba wani abu bane, in har hakan yafi kwanta miki a rai, sai dai kamar ba'a gama jan wutar gidan ba, sannan bamu siyo generator ba."
Goggo da sauri tace "hakan ma ya isa, ba sai anja wutar ba dan acan gidan ma bamu samu wannan darajar ba ni har na rasa ta inda zan soma yi muku godiya."
Ummy tace "dan Allah ki bari, yanzu bari mu barku anan, sai nasa yanzu Sageer ya samo katuwar fitila kafin a gyara wutar gidan, kayanki kuma gobe in Jalila zata zo sai na bada a kawo miki."
Goggo ta kamo hannun Ummy cikin wani irin yanayi na farinciki tace " nagode nagode, sai dai dan Allah ina da alfarma daya dazan nema."
Ummu tace "menene?"
Goggo tace "Jalila tana bala'in san makarantar addini ta islamiyya, bansani ba ko da yanda zakuyi ku taimaka mata."
Ummy tace "basu sata a makaranta ba?"
Tace "basu sata ba, karatun da nake dashi kadan shi na koya mata."
Ummy tai shiru tana tunanin wannan muguntar kafin tace "shikenan zan sanar ma mijinta, hafizi ne na karatu dan da wuri ya sauke alqur'ani zan ji shawarar da zai yanke."
Goggo tace "nagode sosai."
Haka suka fito sukabar Goggo da Lantana a gidan, sai da suka sai katuwar fitila suka kai musu sannan suka fito.
Ummy a hanya ta kalli Sageer tace "Sageer akwai iyayenda in basuyi wasa ba alhakin 'ya'yansu shine dalilin da zaisa su shiga wuta."
Sageer yace "Ummy nikam haryanzu kwakwalwata na mamakin irin wannan mahaifin, wanda san kansa yamai yawa da har baya damuwa da halin da 'ya'yansa suke ciki."
Ameera ta kalli Ummy tace "Ummy nikam dan Allah kumin bayani, wai ya akai Goggo ta zama mahaifiyar Jalila, Mumy fa? Nifa gaba daya na rasa meke faruwa tun jiya nakesan yin tambaya."
Ummy tasa yatsa ta ta tura goshita tace "gulmar me kike sanji? Magana daya dai wannan ce mahaifiyarta me kike nemanji bayan wannan?"
Sageer ya sa dariya yace "Ummy in Ameera batai gulma ba ai ba Ameeran bace."Cikin shagwaba tace "Yaya Sageer haka zakace? Harda wani in banyi gulma ba?"
Ya kara sa dariya yace "To yahkuri ba gulma ba."
Ummy ta kalleta tace "ba wani tayi hakuri, ai dama uwar gulma ce da san jin komai."
Ameera ta kara shagwabewa tace "Ummy Allah ni abubuwan da nakeso in tambaya dayawa fa amma tun yanzu kunsa na kasa."
Ummy tace "sai ki hadiye gulmarki inkin samu Abbanki sai ki tambayeshi."
Tace "shikenan ai nasan Abbana bazai min haka ba..."
Haka sukai ta zolayarta suna dariya cikin farinciki har suka isa gida.
********
A can gida kuwa Hassan tunda ya shiga daki ya zauna a bakin gado yai shiru yana tunani, tabbas gaba daya rayuwarsa ta canza a 'yan kwanakin nan, gaba daya yarinyar nan taki barin zuciyarsa.
Abu daya ne ya fara zuwa mai badai santa kake ba?
Da sauri ya girgiza kai yace "so? Ni? Yarinyar nan?"
Kai ya sake girgizawa alamar ba haka ba yace "tausayine."
Tausayi akan me? Ka tabbatar shi kadai ne? Damuwar da kakeyi fa in abu ya sameta?
Tambayar dake tamai yawo a zuciya kenan, shiyasa ma gaba daya daga ta shigo sai yai gamar yana bacci, ko ya dau littafi wai a dole karatu hakeyi ko ya dau wayarsa....
Ita kuwa daga baya ta sauka falon kasa ta zauna.
Bayan tayi sallar isha'i ne Abba ya dawo, ta gaisheshi ya amsa fuska a sake bai dade da dawowa ba su Ummy suka dawo.
Tanajin dawowarsu ta tashi da sauri tazo taryarsu.
Ummy ta kalleta cikin kulawa tace "Jalila jikin ne?"
Tace "na warke Ummy gashi banyi abinci ba."
Tace "nina hana kiyi, bakida lafiya wake ta ab