u kowa ma ya huta ," " amma kuma idan Ahmad ya sani fa, Aliya ta fad'a ,"," wallahi ko a jikina, ki barmin komai a hannuna , haka dai su ka cigaba da maimaita abinda ya faru, yayin da LAILA zuciyarta fari fes akan abinda ya faru .
A hanzarce ya k'arasa asibitin ,a lokacin Fatima ta jigata , tsananin wahala ya sanya ta farka daga sumar da tayi , suna k'arasawa aka shigar da ita d'akin emergency, ko da likitocin su ka duba , suka gane cewar nak'uda ta kama ta, nan da nan aka shiga bata taimako dan ganin ta samu ta haife abinda ke cikinta, Ahmad da ke safa da marwa , zancen zuci kawai yake yi , lallai duk wanda ya jawa matarsa wannan iftila'in wallahi bazai rabu da duk wanda yayi sanadiyyar fad'awar Fatima cikin wannan yanayin har ya sanyata nak'udar dole, a hanzarce likitan ya fito gami da cewar congratulations, bayan ya mik'a masa hannu " matarka ta haifi yara har guda biyu ma'ana twins , cikin tsananin farin ciki ya ma rasa meke masa dad'i , yama manta da damuwar da yake ciki , ko likitan bai jira ya gama magana ba ya nufi cikin d'akin...............
Please
Share
&
Comments
To be continue............
🌿🌿🌿NUSSAD🌿🌿🌿
🌸🌹KISHIYAR UWA🌹🌸
(True life story)
🍁Daga Alk'alamin Nussad🌸
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
SHAFI NA 45__46
INA BALA'IN YINKU FAN'S, SADAUKARWA GA Y'AN MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION, TARE DA KISHIYAR UWA FAN'S, 😍😍😍😍👌🏻💃🏻
A firgice ya bud'e k'ofar d'akin, a lokacin nurses sun gama gyara ta da babies d'in tsayawa yayi yana k'are musu kallo, yaran kamar ba bakwai ni ba , ganin su yake kamar a mafarki wai ace wannan duk nasa ne , kuma daga tsatson da yafi so , ba shakka yasan Allah kad'ai zai sakawa Fatima amma ba dai shi ba.
Tausayin yaranne ya kama shi, saboda rashin imani , lokacin fitowarsu duniya baiyi ba amma tsabar zalunci sai da aka sanya yaransa suka sha wahala, ya k'udurtawa ransa cewar wallahi kome ake ciki sai ya gano Wanda ya yiwa matarsa haka, kuma yaso kassara masa gudan jininsa.
Tunawa yayi da Mummy hakan ya sanya yayi dialing number na ta , aikuwa bugu d'aya ta d'aya ta d'aga, cikin hanzari ya fara sanar da ita abinda ya faru kama daga dukan da akayi mata , zuwa haihuwar da tayi, sosai mummy ta firgita da jin labari , sunan asibitin ya fad'a mata sannan ya kashe wayar .
A nan kusa da hospital d'in ya fita ya jibgo uwar siyayya , na kayan baby da wanda mamansu zata sanya, bayan kuma akwai a gida .
Ko da ya dawo ya tarar har lokacin suna bacci , cikin kulawa so da k'auna ya k'arasa kusa da Fatima da ke kwance kamar matacciya, anyi mata dressing na wajen da su LAILA su ka dake ta, sanadiyar allurar baccin da likitoci suka mata ya sanya har a time d'in bata farka ba , domin ta samu hutu.
D'aya bayan d'aya ya d'auki yaran hassan da husain, kasancewar nurses d'in sun gama banbanta masa su kowa an lik'a masa sunansa a saman hularsa, Hassan ya d'auka ya masa hud'uba da mahaifin Fatima wato Iliyas ,sannan ya d'auka Hussain ya masa shima kiran sallah da hud'uba ya sanya masa sunan mahaifinsa wato Muhammad, sannan ya jera mata su a kusa da ita .
Hoton yaran ya fara d'auka , sannan yayi posting through WhatsApp, Facebook, Instagram, Twitter da sauransu, aikuwa kan kace me ana ta masa murna Allah ya raya , kiran mummy ce ta shigo wayarsa , hakan y sanya cikin Sauri ya d'aga , ta sanar masa da cewar tana parking space driver ya kawo ta, aikuwa koda ya k'arasa suna tsaye ya musu jagora har zuwa cikin d'akin da suke, sosai hajiya taji dad'in ganin yarinyar ta ta da jikokinta cikin k'oshin lafiya , d'aya bayan d'aya ta d'auka , a nan ya sanar da ita sunan da ya sanya musu , taji dad'i sosai .
Kafin kace kwabo asibitin ya cika da y'an barka , kowa sai sam barka , cikin y'an barkan harda aunty Aisha da Halima k'awar Fatima sai tsiya su ke mata, ita dai Fatima sai murmushi take musu, tana tuna fuskar bak'uwar aunty Aisha, tabbas itace wadda a gabanta LAILA a wanchan karon ma ta illata rayuwarta , kenan a wannan karon ma ita ta kawo LAILA cikin gidan ta kenan , sosai ta shagalta da tunani, daga baya ta yanke hukuncin bazata sanar da kowa ba , zata ajiye abun a ranta, kawai ta barsu da Allah , saboda duk wani abu da ya faru da ita ba kowa ne ya janyo mata shi ba sai KISHIYAR UWA, amma ba yadda zata yi haka zata daure.
LAILA
Achan b'angare guda kuwa, LAILA ta cigaba da lallab'a Aliya akan cewar ba abinda zai faru, ta kwantar da hankalinta, ko yarinyar mutuwa tayi , ba wani abu tunda ba Wanda ya gansu sosai suka shagalta da hira, LAILA sosai tayi murna dan ganin cewar tasan ma Fatima k'arshe sai mutuwa saboda a yadda suka baro ta , kallon Aliya tayi had'i da cewar" kinga Aliy