da ta ga ta saki jikinta sannan ta kira mai k'unshin da zata mata , dama an gyara mata kai dan haka aka fara yi mata k'unshin.
Sai k'arfe biyar sannan ya samu damar barin office, gida kai tsaye ya nufa, ko da ya k'arasa tarba ta musamman ya samu daga LAILA , yayi mamaki sosai amma haka ya biye mata , ya kammala komai , yadda a b'angaren LAILA ta matsu da tafiyar Ahmad haka shi ma ya matsu da ya tafi , har bakin mota ta raka shi , sai da ta tabbatar ya bar gidan sannan ta juya ciki domin fara shiri, cike da murnarta, hmmmmn LAILA kenan.
Yana k'arasawa bakin gidan, yayi horn mai gadi ya bud'e masa, ya shiga , a lokacin su Mummy sun gama jere sun tafi gida, tsayawa yayi ya jera kayansa a wardrobe sosai tsarin gidan ya burge shi , yana gamawa ya nufi gidan Mummy sakamakon kiranshi da tayi akan cewar yaje ya d'auki matarsa ,aikuwa cikin hanzari ya nufi gidan Mummy, uhmmmm sarakan azarb'ab'i kenan.
Ko da ya k'arasa a lokacin angama shirya ta , ba wani dad'ewa yayi ba , mummy tace su tashi su tafi dare ya fara yi , anan fa aka ga abu domin fafur Fatima ta tubure ba inda zata je, koni sai da na mata k'walla , haka ma mummy da k'yar aka lallab'ata ta shiga motar su ka fice daga gidan.
Ko a hanya ma , kukan ta cigaba da yi , yana sauraronta, duk da yana jin kukan har cikin ransa amma haka ya k'yale ta , a hanya ya tsaya ya siya gasashshiya kaza , da fresh milk sannan su ka nufi gidan .
A chan b'angare guda kuwa, LAILA , kwance akan gadon hotel d'in da Aareef ya kama musu, " wallahi baby kanaji da ni irin sannan garab'asa haka, ta fad'a tana duban Aareef da ke fito wa daga cikin toilet da alama daga wanka ya fito" ai baby kad'an ma kikq gani indai ni ne", murmushi tayi, sannan ta tashi ta fad'a jikinshi daga suka cigaba da aikata abinda su ka zo , wa'iyazubillah.
Ko da su ka k'arasa gidan , da kanshi ya mata jagora har cikin gidan, tana lullub'e da mayafi sai k'amshi take yi , a d'aya daga cikin kujerun ya mata masauki, sannan ya nufi cikin kicin da plate ya fito a hannunsa, ya shiga zuzzuba musu, sai da ya gama sannan ya mata umarni da ta sauka su ci tsabar yunwa ce ta sanyata dole ta sauka su ka fara ci duk da a takure take jin ta, bayan sun gama ya nuna mata d'akinta yace ta shiga tayi alwala , bayan ta gama su ka yi sallah , sannan akayi shirin bacci, toh nima daga nan na janyo k'afafuna na fice daga d'akin baki d'aya, saboda kar ace min nayi gulma, wata k'ara da Fatima ta saki ne ya haddasa ni ba shiri na fice daga gidan a miliyan, don tsabar abin tausayi.
Asubah ta gari amarya da Ango.
Ko da na koma lokacin komai ya wakana, Ahmad zaune a gefen gado yana aikin lallashi , ni kuwa nace tunda ka aikata kuwa sai kayi aikin lallashi , komai shi ya mata , sannan ya barta , tayi wankan tsarki, ya shimfid'a mata darduma , ya jasu sallah, albarka kuwa Fatima ta sha ta gurin Ahmad, gani yake duk duniya yafi ko wanne namiji dace , ya kurbu zumar Fatima daidai gwargwado.
Ko da gari ya waye a lokacin Fatima , zazzabi ya rife ta , Ahmad na zaune yana jinya , yaji ana k'wank'wasa k'ofa a hankali ya mik'e saboda kar Fatima ta farka daga baccin wahalar da take yi , yana zuwa ya ga mai gadin Mummy ne ya bashi basket d'in abincin sannan ya juya ya tafi , shi kuma ya koma cikin falo.
Sai k'arfe goma sannan ta tashi a lokacin ya sata tayi brush ya zuba musu abinci , kunun tsamiya ne sai k'osai sai farfesun layan cikin , da lallashi ya dinga bata , yayin da kunya duk ta addabeta , a haka su kayi kalaci , sannan ya bata magani su ka koma bacci.
A chan b'angare d'aya LAILA sai Washe gari ta koma gida , tare da kyautar da Aareef ya mata , aikuwa suna cikin sallama, da Aareef Allah ya jefo da Dr sadeeq , kasancewar ya kira number Ahmad , baya shiga saboda ko shi kansa bai San yayi auren ba , LAILA da ke tsaye bata lura da shi ba dan haka su ka gama duk abinda zasu yi sannan ta shiga gida , da matukar mamaki a fuskarshi ya juya da mota ya bar k'ofar gidan...........
Please
Share
&
Comments
To be continue............
🌿🌿🌿NUSSAD🌿🌿🌿
🌸🌹 KISHIYAR UWA🌹🌸
( True life story)
🍁 Daga Alk'alamin Nussad🌸
🌟🌙🌙🌙🌙🌙🌙🌟
*🌙✨MOONLIGHT WRITER'S ASSOCIATION🌙✨*
https://m.facebook.com/Moonlight-writers-association-109698351308376/
*'''We are the moonlight writers we shine all over the world.''🌍'* ✍️✍️
بِسم الله الرحمن الرحيم
~~~~~~~💞💞~~~~~~~
SHAFI NA 43__44
Toh haka dai Ahmad ya kwashe kwana bakwai a gidan Fatima, suna kwasar amarci da soyayya, tun Fatima najin kunya har ta saba , ta sake tare da taimakon k'awarta Halima, sosai take wayar mata da kai, aikuwa tayi amfani da shawararta ta, sai da ya kammala kwanakinsa, sannan ya koma gidan LAILA badan ya so ba.
A haka dai zaman na su ya kasance cikin walwala, da soyayya, yayin da a b'angare d'aya kuma zaman LAILA da Ahmad, ba'a cewa komai, ita dai t