utukar ganin bayan auren sunje wajen boka ita da Abu ya basu tabbacin cewar zaa fasa auren kuma da d'iyarta zaayi , amma me har ana I sauran kwana biyu biki ba abin da ya sauya .
A daren d'aurin auren ne Ado ya samu mahaifiyarsa da zancen shi fa ya fasa auren Fatima Abu yakeso , sosai tayi mamaki da jin haka , kuma tabbas tasan Asabe ce tayi aiki dama ance abokin mugu , mugu ne .
Ranar d'aurin aure da safe lokacin kowa ya hallara a inda za'a d'aura auren komai ya gaba daidaituwa aka sanar da cewar an sauya ango yace Abu yakeso ba Fatima ba , sosai mutane sukayi mamaki aka d'aura auren Abu da Ado cikin sadakin kud'i naira dubu goma.
A lokacin da aka d'aura aure Fatima tana gida tana sharb'ar kuka saboda batasan auren dan kawai anfi k'arfinta ne ba yadda ta iya , mata kuwa aikinsu suke tayi kowa na murna inna Asabe kuwa da suka san me yake faruwa Murna sukayi ta yi .
Marok'i ne ya fara sanarwar d'aurin aure! An d'aura auren Adamu da zainabu akan sadaki naira dubu ashirin! Yana ta sanarwar har ya shiga cikin gidan yana sanarwar, matan da ke tsakar gidan mamaki ne ya cika su jin abin da marok'in ke fad'a .
Fatima da take zaune a cikin d'akin abin da kunnuwata suka jiyo mata ne ya sanya ta fito da gudu domin ganin abin da ke faruwa.......
Please
Share
&
Comments
To be continue.......
🌿🌿🌿Nussad🌿🌿🌿
🌸🌹KISHIYAR UWA🌹🌸
(True life story)
🍁Daga Alk'alamin Nussad🌸
GODIYA GA ALLAH DAYA BANI DAMAR CIGABA DA RUBUTUN LITTAFINA , BAYAN DAN HUTUN DANA DAUKA BISA GA UZURIRRIKA .
A YAU INSHA ALLAHU ZAN CIGABA DA RUBUTUN LITTAFIN KISHIYAR UWA FATANA ALLAH YA YI MANA JAGORA
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
🌹🌹🌹🌹🌹
🌸🌸🌸🌸
🌹🌹🌹
🌸🌸
🌹
SHAFI NA 1️⃣1️⃣-1️⃣2️⃣
Koda Fatima ta fito ganin abin da ke faruwa , ji tayi wasu mata daga k'ofar d'akin girki suna magana ,d'ayar matar ta dubu y'ar uwarta " ke ni kuwa hansai bakyaji min abin da kunnuwa na ke ji ta fad'a tana k'ara kasa kunne", matar da aka kira da hansai ta ce" ashe dai bani kad'ai ke ji ba , yau naga lalata da idona, mu da aka kira mu bikin wannan yarinya Fatima ta ya ya auren ya sauya kan wannan fitsararriyar yarinyar, ta fada tana sallallami had'i da tafa hannayenta".
Ita dai Fatima ji tayi kamar tayi sujjadar godiya saboda dad'i , surutai ne ya fara tashi a tsakanin mata , wannan ta fad'i nata wannan ta fad'i nata, Baba Muhammadu k'anin marigayi malam Iliya mahaifinsu Fatima ne ya shigo gidan ransa a matuk'ar b'ace , d'akin inna Asabe ya shiga da sallama , mutanen ciki suka amsa , tambayar Asaben ya yi sai gata ta fito, sadaki kawai ya mik'a mata na d'iyarta sannan ya sanya kai ya fita cike da takaici, yana fita ta wani rangad'a gud'a sannan ta kama habaice habaicenta , niko na ce kyayi kya gama .
Achan b'angaren Fatima kuwa d'akinta ta koma cike da jin dad'i, tana cikin wannan farin cikin Baban nata malam muhammadu ya Shigo d'akin tsammaninsa ya same ta tana aikin kuka saboda yasan ya zuwa yanzu tasan koma da yake faruwa , amma me sab'anin haka ya tarar domin kuwa fuskarta ba abinda take fitarwa sai annurin haske da murmushi, tashi tayi , tayi masa sannu da zuwa yana amsa, nasiha mai ratsa zuciya ya mata, daga bisani ya shaida mata abubuwan da suka faru , yadda yaga bata damu ba hakan yayi masa dad'i sosai , ya yi mata sallama ya fita ya koma wajen y'an d'aurin auren.
Toh a haka aka daura aure su inna Asabe baki har kunne yarinyarta ta samu mai kud'i , Wanda yake fita birni dama hakan tafi so ace yau d'iyarta tafi ta kowa sa'a a k'auyen , haka dai aka k'araci bikin anci an kuma sha biki kam sam barka amma fa Fatima tasha habaici wajen inna Asabe da k'awayenta har ma da zainabu da k'awayenta dare nayi aka kai amarya gidan mijinta da zummar sati d'aya zasu yi su tafi Lagos sai mu ce Allah ya bada zaman lafiya ya kad'e fitina amin .
Lokaci nata tafiya bayan anyi biki amarya su ka tf da mijinta Lagos , a haka lokaci ke ta tafiya , cike da k'alubalen rayuwa a yanzu shekara d'aya kenan da bikin zainabu da Ado , a yayin da Fatima take cikin tsaka mai wuya , cin zarafi ,kyara , habaici, duka , zagin cin mutunci, ba Wanda bata fuskanta ba daga mahaifiyar ta ta inna Asabe, ga wani cin zarafi da y'an k'auyen keyi mata , duk inda suka ganta zancensu d'aya tak'i aure , wasu ma har cewa sukeyi tana zaman karuwanci ne kawai ganin mahaifinta baya duniya , dama dai sauran maganganu barkatai , haka take d'auke kanta daga wad'annan habaice habaicen wani zubin inna Asabe da k'awayenta ne zasu taru a gidan su ci mata mutunci son ranta, ga aikatau iri iri bata hutawa , ita kuwa inna Asabe taci mai kyau tasha mai kyau ba abinda ya dame ta saboda y'arta tana aiko mata da abin duniya , Fatima kuwa sai tayi sa'a sannan ta samu abinci taci say d'aya a rana , kuma duk wannan halin tsananin da take ciki bata tab'a tarar kowa ta fad'a mishi ba , gashi samari yanzun basa zuwa wajenta mutane suka dinga tunanin ko shafar aljanu ce , ko kuma dan