NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 12 of 44

daga d'akinta da kaya a hannunta , watso mata tayi a fuska , " gashi nan ki wankemin saboda kayana sun taru babu masu wanki a cikin" dubanta Fatima tayi tare da cewa " amma ai kinga Baba bashi da lafiya ko ta yaya zan iyayin wanki a halin da nake ciki , " au bazakiyi ba kenan, to wai ma da kike cewa Baban bashida lafiya ina ruwana da rashin lafiyar tasa , kinga in zakiyi min wanki kiyi in kuma kika k'iyi kema kinsan sauran banza kawai, ta juya ta shige cikin d'akin na ta , tabar Fatima baki bud'e , babu yanda ya iya haka ta d'ebi kayan ta wuce ta wankesu, ba ita ta gama ba sai da akayi sallar magariba , kana ta gama wankin tsaf saboda akwai su da yawa. A chan asibitin kuwa an bawa malam gado , dan ciwon nashi yayi tsanani dan haka kiri kiri da aka ce inna Asabe zata dinga kwana ta nuna itafa bazata iya ba , malam muhammadu ne ya tafi da kansa ya maidata gida kana ya dauko Fatima domin ya fuskanta da ita zanta iya juriyar kula da malam d'in , aikuwa koda akace ta shirya ba musu domin itama tana buk'atar ganin mahaifin nata , da Asabe ta so ta hana ganin in Fatima ta tafi to fa babu mai aiki a gidan haka zalika babu mai zuwa mata tallah ya ya kenan , amma da yake dama ba shiri sukeyi da muhammadun ba haka yayi Jan ido wa Asabe ya tafi da Fatima asibitin, ko da taga mahaifinta halin da yake ciki kuka ta kamayi da k'yar Baba Muhammadu ya lallasheta , da cewar ai dana samun sauk'i in taci gaba da kuka zai maidata gida , jin haka ya sanya tayi shiru ba shiri, a haka suka kwana bata samu damaryin bacci ba har asubah a sannan ne malam Iliya ya farka ruwa ya nema aikuwa da Saudi Fatima ta k'arasa tareda taimakon baba muhammadu su ka bashi ruwa" sannu Baba" abin da ta iya furtawa kenan sai hawaye , da Sauri ta goge da ta tuna da sharad'in da k'anin baban nata ya fad'a mata , murmushi malam Iliya yayi mata tareda shafa kanta da hannunsa wanda babu ruwa a jiki da muryarsa da bata fita yace " Allah ya miki albarka d'iyata " ," amin baba" tayi furucin a sanyaya , to bayan su taimaka masa yayi alwala suka jinginar da shi yayi sallah , kana suka soma hira har wayewar garin snnan ya koma bacci. "Wallahi in baki fito daga d'akin nan ba ko ki kuka da kanki" , Asabe ce ke wannan hargagin wa Abu , karar bud'e k'ofar da k'arfi shiya sanya Asabe ja da baya " wallahi inna bazanje aike ba gwarama ki fita da kanki kije ki siyo, hana ayi ta damun mutane aikin banza aikin wofi" Abu ce tayi maganar ta karkad'a kafad'a, jawota Asabe tayi aikuwa itama ta kamata da kokawa sosai sukeyin dambe , ni kuwa abin nema ya samu jinayi kamar na kad'a musu ganga safiyi da kyau sosai" innalillahi kai kai kai menene haka" Baraka ce tafi wannan furucin tana tafa hannu ," ki barni in ji mata ciwo yarinyar nan kamar bani na haifeta ba wai har nace ta zo taje aike aike amma ta k'iya ", wallahi bazanje ba ehe ta shige d'aki had'e da Santa sakata , Baraka ce ta dubi Asabe ke ni ba wannan ba ma wai ya batun auren ne saboda yaron nan ya matsamin " ," eh na sanarwa da malam din ya amince yanzu saura saka ranar biki kawai " Asabe ta fad'a da yanayin alhini a fuskarta" ke malam din ma fa bashi da lafiya hana asibiti," " meya sameshi to Allah ya k'ara afuwa" bata saurari me Asabe zatace mata ba ta juya ta fita . To har azahar sannan Asabe ta gama aikin gidan duk ta wahala ta jigata ta sauya kamanni, Rana gamawa Abu tazo da d'iba abincin ta kuma shigewa d'aki ta banko k'ofa . To kwanan malam uku a asibiti a lokacin ya samu sauk'i ba laifi dan har ana tunanin za'a sallameshi , Fatima sosai tayi murna ga bisa samun sauk'in mahaifinta , domin shi ne a yanzu yake matsayin jigo a rayuwarta , a daren rana ta hud' u ciwon malam ya dawo sabo sosai hankalin fatima ya tashi kuka takeyi sosai , hankalinta ya tashi gashi baba Muhammad ya fita inna Asabe kuwa tunda ta tafi bata dawo ba tun ranar da aka kawo malam din, ta yunk'ura zata tashi ya rik'e ta "tsaya d'iyata mafi soyuwa a gareni" , wasu zantuttuka masu kama da wasiyya ya shiga yi mata wad'anda bata ganewa , nasan dai nayi mini laifi ban sanar da me ko asalin wacece ke ba hak'ik'a nasanki da hak'uri da juriya to kick gaba daga inda nasanki hak'ik'a akwai jarrabawoyi da yawa da ya kamata ki cinyesu ina fatan zaki cinyesu , kiyi hakuri da duk halin da kika tsinci kanki a rayuwa , kiyi taka tsantsan a gaskiya auren da akeson yimiki banasonshi amma saboda gudun wannan ranar da zan tafi in barki ya sanya na yanke hukuncin da kiyi aure amma d'iyata in kin samu miji ko bayan raina kiyi aure hak'ik'a inason kiji dad'in rayuwa ina mini wasiyya kiji tsoron Allah", a lokacin ya bata labarin mahaifiyarta sosai takeyin kuka sosai dana ashe yadda tayi hak'uri mahaifiyarta ta fita , lallai itakam batasan menene zai faru ba , muryarsa a lokacin ta farayin sanyi . Allahu Akbar a take a lokacin Allah ya amshi rayuwar malam Iliya Allahu Akbar said dai mice Allah ya jik'an musulmi jin shirun da Fatima tayi shi ya fargar da ita halin da ake ciki da gudu ta fita waje dan sanarwa da doctor halin da ake ciki , kafin ta k'
🏠