NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 78 of 146

da abokan arziki zaki iya tallata masu idan kin kawo mutun goma suka shiga na 10k kinada package din 5k Idan kin kawo mutun goma suka shiga na 5k kinada package din 3k. Zuzeam ventures 08144015291 ******* Cikin gaggawa da tsananin sauri babbar jakadiyarta mai suna fatto ta iso tana riqeta hannuwanta na rawa da kakkarwa ta riqeta tana sanar da bayin suyi gaggawar gyara dakin da zatai naqudar. A take kuwa duka bayin dake babban bangaren nata suka hau shirin gaggawan tarban haihuwar, Ruwa da wasu abubuwan al’adah suka fara gaggauta hadawa wasu kuma na gyara Wani lafiyayyan daki daya a cikin tarin dakunan dake bangaren nata, Jini ne sosai yake zubar mata Wanda ya saka hankalin fetto da Sauran manyan bayin nata tashi take akai gaggawar isa da ita dakin da akaiwa shirin karban haihuwar tata aka kwantar da ita idanuwanta a rantse cikeda wata mummunar azabar datake sake tsananta tafasa jininta dake wata irin tafarfasa, Budewa idanuwanta tayi da sukai wani mummunan ja zufa na jiqata ta sako wani azababben nishi tana bude baki da karfi cikin azabar datake ratsata tace ‘Sultan yasan da cikin kuma yaci gaba da kwanciya da ita a tirakarsa……. Wishmah a Masarautar BOYEM yanzu? Qarni qarni sun shude harma tarihin samun wishmah a BOYEM yana shirin shudewa shine yanzu rana tsaka sabuwar wishmah zata bayyana Akan sultan YASAR? Me take dashi wannan imebetin? Wace ce ita? Tayaya zata samu matsayin wishmah dake kusan nuni da itace macen datake zuciyarsa fiyeda matansa na aure……… Wani Ihu mai tsananin qarar gaske ta sake jikinta na wata irin jijjiga da fizga, Azabar naquda takeji tana ratsa dukkanin qasusuwan jikinta amma kuma baqin cikin dayake ratsa jininta shi takejin yana Neman kasheta dan kuwa Ayau da ba tata naqudar takeyiba wlh tallahi bazata Bari Ayanah ghaz ta haihuba, Wani irin yunqurin azaba ta fara gabobinta na amsa wata kakkarfar azaba sbd bazata iya yadda Ayanah ta rigata haihuwa ba dan kuwa a tabbacin bokayenta sun tabbatar mata da duk haihuwar da zaa fara a BOYEM yanzu to tabbas namiji ne taurari sun buga sun buga sun tabbatar da hakan dan haka ko zata yage saita turo abinda yake cikinta ya fado duniya, Cikin tsananin kulawa babbar yarta ta iso bangaren cikeda damuwa da kulawa ta iso ta gefen mahaifiyars tata batareda tana ganin wasanta dake rufe kare da wani babban kyalle green su fetto da likita mace daya da suka kirawo sai babbar baiwarta daya suna kokarin karban haihuwan duk sun hada Wani irin gumi, Nauyi da azaba tareda rikice wa naqudar tayi wadda take sake saka jini fitowa da sauri fetto ta kalli HAILE din wadda azabar tayiwa yawan da tana kokarin ficewa hayyacinta ta bude baki zatai magana cikin girmammen baqin ciki da ukuba HAILE tace bata bawa kowa ikon ce mata komai ba matiqar ba haihuwan suka tayata yiba, Likita data dago yin maganar dole suna buqatar kiran Sauran likitocin da zasu taimaka mata Jin abinda Hailen ta fada ya sakata yin shiru tana hada zufan tashin hankali sbd akwai Sauran time dan kuwa service dinta baima gama budewa ba dan haka sunada aiki sosai ga naqudar bame sauki bace yakeyi tinda shock ne Kai tsaye ya tado naqudar, Fetto Kai da kawo ta fara tana fitowa tana komawa cikin tsananin tsoro da tashin hankali me girma ga Masarautar tayi Wani irin tsit babu motsin komai bare kowa alaman duka manyan BOYEM sun taru a fada jiran naqudar Ayanah ghaz wadda itace wadda kaf BOYEM yanzu ake jira dan haka a kakkarfar doka da baa takewa ta Masarautar gabaki dayanta shine duk jinin BOYEM idan zaa Haifa Ana fara naqudar sa babu me sake fitowa bare kaida kawo tsit akeyi har sai ta sauka dan Kai tsaye duk Wanda tsautsayi ya sakasa fitowa ko kaida kawo a hanya cire kansa daga gangar jikinsa ya halasta, Dan haka ne Ayau dinma babu motsin komai bare hayaniyar komai koina tsit ne tamkar babu dan Adam ko daya a cikin masarautar BOYEM din, Duka tarin bayin daka bangaren Haile sun gama shirin tarban abinda zata Haifa dan haka a tsaye suke qyam babu kowane motsi dayake tashi suka anan din sai fetto daka Kai da kawo kaman zata rasa hankalinta ta zare, Zufa sosai take hadawa gashi ba ikon magana so take taje ta isarwa sa sultan labarin naqudar Haile amma ba damar fita dan fitarta daidai take da kwananta kabari Ayau din dan saita bar duniya dan haka babu damar fita, Su kansu bayin dake bangaren duka babu Wanda ma yakeda ikon motsi bare fita zuwa isar da sako dan haka ta rasa yaya zatai da rayuwarta fa naqudar sai abu daya ake kwata kwata babyn bai fitoba, Ita kanta likitan kokarin tsayar mata daya jinin tayi da taimkon da zata iya bata amma dole haihuwa sai lokacin da Allah yace babyn ya fito zai fito dan haka dukansu zufa suke hadawa ba qarami ba suna rasa abin yi har HAILE din tayi Laushi sosai amma taqi yadda kowa ya tsaya hutawa sbd baqin taurin ranta Akan kada Ayanah ta rigata haihuwa, Tana tsananin buqatar likita amma babu me ikon fita dan kuwa koda Ka isa ka isar da sako tabbas zaka karbi hukuncin barin duniyar Ka dole Shiyasa kowan
🏠