NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 137 of 146

su sbd tsananin biyayyarsa da rashin hayaniyarsa. Saida yayi shekara kusan goma a hannunsu tukuna sukasan asalin jinsinsa da tintini boukar ya fahimta amma bai nuna masa ba sbd son qure lamarin Wanda baisan ina ze tsaya ba dan haka ya fuskunci hukunci me tsanani a gurinsa kafin kuma daga karshe ya barsa a macensa cewa shine hukuncin sa haka zaici gaba da zama tamkar dan daudu. Baiji ciwo da Zafin hukuncin ba sosai sedai Ka quncin sa daya dawo sabo na rashin yan uwansa a rayuwarsa dayake ganin batada Sauran amfani a gurinsa, Yanayin alaqar sa da ayshaah sauyawa tayi sbd jinsinsu daya bayyana ba daya ba dan haka ta rage shige masa sosai hakama ta Dena bayyanar da inda be kamata ba a jikinta indai suna tare sbd kiyaye dokar addini. A hakan sukaci gaba batareda sun sauya masa tako wace hanya ba ko kadan, Kaf garin sun San Nurat a matsayin bawan ahalin da shine bawan da zai zama na ahalin me zuwa dan kuwa idan har boukar ya mutu Nurat yana cikin gadon da zaa raba maana shi Kansa abinda Wani ze iya gada ne a gurin rabon gadon Wanda yan uwansa keta lissafi sbd arzikinsa yayi wata irin sake habbaka ya tara dukiya ke yawan gaske data saka yarsa taje rayuwa tamkar sarauniya a fada, Da farko Bayan angane Nurat namiji ne ba mace ba mutan gari sun so korarsa sbd jifansa da ihu aka ringa yi masa daga kasuwa da aka aikesa Wanda Koda ya iso gida sun masa mummunan illar data sauya masa kamanni sosai sbd jifar ta fasa Kansa da fuskarsa amma a hakan ya iso gidan baya ko gani sosai sbd jinin daya rufe idanuwansa. Da karfin dukiya boukar yayi amfani ya hana a kori Nurat din amma kuma tin daga wannan lokacin Nurat ya zama abin qyama da hantara tareda jifa a cikin mutane a duk lokacinda zai fita gashi har lokacin shigar mata yakeyi, Tsananin tsana da qyama tareda hantarar dayake fuskanta a rayuwarsa tsawan shekara kusan uku ya saka rayuwarsa gabaki dayanta komawa asalin baqin ciki da qunci dan haka sai abin ya fara taba zuciyarsa da daman bata taba fita tsananin qunci ba. Wasu bayin boukar ya siyo guda biyar masu karfi dan gadin gidansa da ako Yaushe ake kokarin kawo harin Kai karshen rayuwar Nurat din Wanda kaf garin suke ganin mugun abu ne a cikinsu zama da zabgegen namiji a cikin Kayan mata dan haka koda be bar garin ba to zasu kashesa dan zamansa a garin tamkar zunubi ne. Cikin wannan fitinar dake tashi koyaushe yan uwan boukar dake harin rayuwarsa suka shige sbd samun biya da cimma burinsu na shekaru masu yawa akansa sbd a yanda Nurat ta zama rayuwarsa da ‘yarsa bazasu iya rabuwa dashi ba dan haka suna samun ya fara shirye shiryen barin garin da Nurat dan komawa Wani garin suyi rayuwa hankali kwance tinda yanada dukiyarsa me yawan gaske. Ana cikin wannan halin rana tsaka kwatsam cikin dare kawai aka cinnawa bangaren abincin boukar dake gidan wuta inda tarin dukiyar abincin sa take me yawan gaske buhuhuwan hatsin da dukiya ce me tsananin gaske, Fitowa boukar din yayi cikin duhu da hayaqin daya gauraye gidan har Baka ganin komai yana kokarin isa bangaren idanuwansa da kunnuwansa sukai masa mummunan ji da ganin daya tabbatar masa da halin yan uwansa dayake zargi na shekaru masu yawa dan haka da sauri ya juya cikin hayaqin jikinsa na rawa zuciyarsa na Wani irin radadi da firgici sbd lamarin Yazo masa a bazata. Fada ne ya fara kaurewa da hayaniya tareda ihu a gurin kashe wutar wadda duk da tsakiyar dare ne amma take mutane da suka cika gurin da sunan kashe wutar da kuma son qaddamar da nufinsu a cikin hayaniyar kashe gobarar na kashe Nurat su kuma yan uwan boukar kashe sa dan hakanne ma suka fada sun tada wutar yanda zaa hargitse ana ihu da hayaniyar kashe wuta su kuma sukuma su aikata aikinsu tareda sace dukiyarsa dan haka basu taho da shirin barin ko ‘yarsa ta rayu ba bare bawansa. Fada aka fara tareda sare sare Ana fidda jini me yawa sbd bayin dake tsaron gidan da sukaga alamar fitina a tattare da kashe wutar dan haka suka fara hanawa sedai ko gama rufe baki na farkon beyiba suka rufu a Kansa suka sassarashi suna cewa shi bawa ne bai isa ya basa umarni ba sedai su su basa. Jin hayaniya da Ihun kashe karshen daya dauki gari ya saka boukar daya dauko makaminsa dakatawa ya juya ahankali ya kalli kofar dakin ayshahh sai kawai yaji tinaninsa ya sauya ko yayane yanason ‘yarsa ta rayu dan haka ya nufi kofar dakin da Nurat yake kwana yana zuwa Kai tsaye shiga dakin yayi ya tadashi da karfi tareda dagosa daga kwancen batareda yace komaiba ya riqo hannunsa da karfi suka fito tsakar gida yana sake shiga tashin hankalin hayaniyar da Ihun daya qarasa gauraye gari. Abaas na fitowa yanda wutar take ci da Ihun da akeyi ya sakasa jin Kansa na Juyawa zuciyarsa na bugawa da karfin gaske komai na yanda ya faru garinsu yana dawo masa sabo. Wani irin Zafi da tiriri yaji yana tasowa daga zuciyarsa yana gauraya jininsa komai na sake dawo masa tin daga gawar magaifiyarsu da suka fara rasawa. Rawa jikinsa keyi kowane irin radadin daya dandana a baya yana dawowa yana zama kuzari da fushinsa dan h
🏠