nnan burin nasa Akan NUAB din ya cika kafin ya nemi kusanci da ‘dan nasa dayafi masa duniyarsa gabaki daya.
Cikin sautin daya saka fadar sake daukan tsit NUAB ya bude Baki muryansa ta shiga kunnuwan duk Wanda yake gurin kaman saukar Aradu yana juyowa yace
‘Waye yaga ya kamata a aika bayin Amminah kirana???
Rufe idanuwa sultan yayi a hankali Wani radadi na ratsa zuciyarsa na yanda ‘dansa ya zabi kasa masa magana a bainar mutanen fada da suma duk sukai tsit sbd kafe fadar da Yaransa sukai da ido ba ko kyaftawa kamar robot suna jiran Wanda zai motsa bada amsar shine su fasa kansa da bindigar dake hannuwansu ko Jeho masa wuqar da zata tsaga kansa biyu dan haka ganin sultan baice komai ba har lokacin kallan NUAB yake son dayake masa yaci karfin mulkinsa da matsayinsa dan haka sukai shiru babu Wanda ya dago tukuna dan kuwa duk karfin mulkin BOYEM aka fasa kan mutum da bindiga kafin masautar ta dauki mataki ko nuna ikonta da zafinta Akan hakan andai Riga Kai an kasheka a banza da wofi ihu ne kawai ze biyo Bayan hari gashi da alama kafiran samudawan thugs din dake tsaye basu San dokokin masarautarba tukuna dan haka ba wata bata lokaci zasu aikaka ba shiri.
ASIM ne ya motsa cikin tsananin mamaki da baqin ciki me girman gaske ya miqe shima ganin NUAB bai durqusaba ya kalli NUAB din ransa na tsananta tafasa da quna mai tsanani ya bude Baki zaiyi magana NUAB din ya sake bude Baki da mahaukaciyar muryan data saka ASIM din ja da baya cikin sauri
‘Waye ya nuna wannan rashin daar ga mahaifiyata????
Aleeyyy……….
Cikin karfin murya datake tattare da umarni da iko mai karfi Sultan ya Katsesa sbd hanasa abinda yake niyar yi koma menene yace
‘LEUL NUAB ALMAZZ ka nutsu kasan inda kake,
A gaban me BOYEM kake,
Nine me mulki a nan ba kaiba,
Nine me fada aji anan ba Kai ba
Nine Wanda ya isa ya kira kuma dole a amsa,
Sake kallan jikinsa sultan yayi cikeda bacin rai kafin yace
‘Nan fadar BOYEM ce ba gurin wankanka ba dan haka umarni ne ka koma Ka sake shiryawa fada zata sake nemanka amma Ka sani hakan da kayi na yanke maka fita Masarautar BOYEM bisa umarni me karfi sai Bayan wata daya zan buqaci ganinka’
Da mamaki me karfi da shakkar dake cikeda zukatan yan fadar kowa ya dago ya kalli sultan sbd zazzafan furuci suke jira daga garesa da hukunci me Zafin gaske amma suma tsananin shock da mamakin da suka kasa fitowa a cikinsa na ganin tantirancin karshe ganin idonsu ya saka suka bazasu iya cewa komai ba ko yin komai sai tinani da nutsuwansu ya dawo daidai jikinsu tukuna dan haka barin fadar a watse meeting din suke buqata yanzu suje su sako tinani,
NUAB kuwa juyowa yayi cikin nutsuwa da sabuwar tafasar datake cin ransa zai kalli sultan sai kuma ya fasa ya juya yana barin gurin sbd bayason jijjiga duniya da ikon sultan din a gaban mutanen da ikonsa yafi komai a duniyarsu.
Yana Juyawa gabaki daya bayi da securities din fadar suka sake zubewa qasa suna sauke kansu jikin bayi na tsima,
Su aleey ma Juyawa sukai suna bin bayansa sultan ya zubawa Bayan NUAB din idanuwansa yana kallan sunan GHAZ din dayake Baro Baro bayyane a tsakiyar bayansa daga sama.
Kaman yanda ya taho haka aka daga masa umbrella ta basa kariya daga Zafin rana hakama shades dinsa na rage masa hasken rana ne da zai keto a cikinta,
Har suka fice sukai nisa babu Wanda ya motsa saida suka bace wa fadar gabaki daya tukuna aka ringa sauke Numfashi me Zafi da bacin rai me tsanani musamman ASIM daya kasa motsawa daga kallan inda suka wuce din idanuwansa jajir da sbd tsananin ja da bacin rai da baqin cikin dayake ciki har wasu ruwa ruwa suka cike idanuwan fuskarsa tayi jajir hannuwansa na dan rawa ya saukesu yana juyowa ahankali ya fara bin palace officials din wato manyan fada da kallo daya bayan daya yana debe musu albarka a zuciyarsa tareda Jin zazzafar tsanarsu da baqin cikin ganinsu ma a gabansa sbd shiga rudin da sukai har suna kasa cewa komai a fadar da sun isa su yankewa ‘dan mistress kowane irin hukunci,
Wasu yawu masu daci na baqin ciki ya Hadiye yana dauke idanuwansa daga kansu ya dawo da kallansa kan sultan Wanda tin kafin ASIM din yayi magana yace ya tada zaman fadar na yau sai kuma wani lokacin.
Cikeda girmamawa da son barin fadar su shaqi iskan nutsuwa a waje kowa dake fadar suka zube qasa a hankali suna masa a huta lafiya.
Koda ASIM ya zube qasan shima zuciyarsa kaman zata fado yake jinta tsabar baqin cikin sultan da duk Wanda yake fadar dan haka har sultan ya bar fadar ta kofar da shi kadai yake bi ASIM bai dago ba,
Sultan na ficewa aka fara ficewa daya bayan daya daga fadar babu Wanda ya samu cewa dan uwansa komai har suka watse,
ASIM ne yayi na qarshen fitowa tareda babban yaronsa Salman Wanda shima zuciyarsa taje cikeda baqin cikin dayake kusan na ubangidansa haka suka bar fadar Kai tsaye suna nufar bangaren HAILE.
A kofar bangaren da babu me wucewa sai jinin BOYEM da bayinsu mata kadai,
Tinda ya tinkaro bayin dake bangaren suka ringa zubewa qasa kansu a qasa suna masa Bar