NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 114 of 146

mulkin shi a hana masa dan babu ta yanda dan taadda zaiyi mulkin BOYEM baa taba ba kuma bazaa taba farawa ba. HAILE ma kusan bazasu taba gane abinda take ji a zuciyarta ba sbd har abada indai NUAB ALMAZZ yana raye batajin akwai ‘dan da sultan zai so kamarsa duk da baya tareda NUAB din shekara da shekaru amma hakanan take Jin bai taba Dena sonsa ba kawai abinda ya sakata kwantar da hankalinta shine koda yana sonsa baya tareda shi yana tareda ‘danta ne kuma gaggawar datake yi shine a Dora ASIM kafin ranar dawowan NUAB tayi gashi yanzu ya dawo batareda burinta ya cika ba dan haka yanzu sabon yaqi ne garesu su dukansu Akan tabbatarda burinsu ya cika kota halin yaya. *****Se karfe goma da mintina ya Baro bangaren Amminsa Bayan yaci abinci tareda ita cikeda kwanciyan hankali sun samu kasancewa da juna yanda yakeso tukuna ya fito ya fice. Lafiyayyan gyaran da akaiwa bangarensa ya saka yana zuwa Kai tsaye bedroom dinsa ya nufa Wanda yake da Wani palon hutawansa a ciki kafin asalin bedroom din. A jikin bangaren nasa akwai manyan bedrooms guda biyu da sukeda girma sosai da toilets a ciki anan Yaransa suka sauka aleey kuwa bedroom daya dayake cikin bangaren nasa ya sauka dan haka dukkaninsu shigewa sukai sbd lokacin hutun LEUL ne. Wanka yayi da dukkanin abinda ya saba amfani dashi sbd babu abinda yake amfani dasu da aleey bai siyo ba baa. Dogon wandon bacci na lebarto ya saka mai wani irin santsi da Laushi sbd tsadarsa sai farar rigar wandon Kwantawa yayi ransa da ruhinsa cikeda nutsuwa take baccin hutun dayake buqata ya daukesa. Gabaki daya bangaren da zagayensa tsit yayi sbd Yaransa da suka tabbatarda hutawa yakeyi babu kowace hayaniya da ake buqata. Daga shi har Yaransa Hutu sukeyi Bayan an bada cikakkiyar umarnin kada Wanda ya tinkaro bangaren. Acan fada kuwa kowa ya cika duk wani babban masarautar yana cikin fada Zaune, Hakama duk Wanda yake gari ko qasar datake kusa da BOYEM indai jinin BOYEM ne sun iso suna cikin masarautar wadda ta dauki dumi dan kuwa a cike take da masu fada a ji na mulkin BOYEM, Shi kansa sultan Bayan dogon lokaci daya dauka kafin fitowansa ya fito daga karshe Bayan kowa ya gama Halarta kenan shi kadai ake jira da LEUL din Wanda baima San mesuke yiba, Zaman fada da meeting din zafi ya fara dauka Wanda ya saka sultan yake sake jin baiyi danasanin aika dansa ba harma ya zama koma menene ya zama yanzu din dan kuwa a bayyane wata irin zazzafar qiyayya ce yake gani tako ina a idanuwa da kalaman duk Wanda yake fadar Akan sai hukunci yahau kan duk Wanda ya taka dokar Masarautar BOYEM koma wanene. Sultan da abu dayane yake cikin zuciyarsa yana Juyawa shine rashin zuwan NUAB din garesa Bayan shigowa sa masarautar da shine yake mulki da ikonta hakama shine uban daya haifesa komai Zafin kansa da ikonsa wainda a gurinsa cikin jininsa ya gajesu, Dagowa yayi ya kalli taron manyan qasar BOYEM din gabaki dayanta da idanuwansa da tsananin zallar mulki da ikon dayake jininsa yana bayyana, Umarnin suke jiran ji dan haka akai tsit Ana kallansa tareda jiran abinda zai fada kowa zuciyarsa har rawa takeyi sbd jiran umarnin da sultan din zai bada. ASIM da idanunwansa sukai jajir zuciyarsa har wani fizga takeyi ya kafe sultan din da ido yaja baza kunnuwansa jiran abinda zaa fada, Bude bakin sultan umarnin kiran LEUL BOYEM ya bada tareda tabbatarda umarni ne me karfin gaske. Dan aike Koda ya isa tin daga nesa ya zube qasa bakin kofar bangaren yana daga muryansa ya isar da sakon cikin tsananin girmamawa. Dukkanin sakonsa a kunnuwan Yaransa ya isa amma babu Wanda yakeda niyar isar da sakon sbd lokacin gurinsa bai qareba dan haka manzon sakon yana zube a qasa bai tashi ba sbd Sai an amsa masa sakon zai tashi koda kuwa zai kwana ya wuni a hakan. Shiru shiru ba dan sako Wanda ya saka fadar sake daukan zafi babu Wanda ya iya cewa komai sedai xukata sun dauki Zafi. Awa kusan biyu manzon sakon ya shafe a durqushe cikin rana kafin me BOYEM din ya tashi baccin sa Kai tsaye ya shiga toilet yayi wanka ya bata lokaci sosai kafin ya fito daure da towel fari qal daidai nan wani manzon sakon ya sake isowa sedai wannan Karan bayi biyu ne daga bangaren mahaifiyarsa aka turo Wanda hakan ya sakasa Dakatawa cak daga abinda yakeyi sbd bayin saida suka gabatar da kansu suka isar da sakon ya kuma San me ake nufi da aiko bayin mahaifiyarsa Wanda take zuciyarsa ta fidda Wani irin Numfashi me dumi ya ajiye towel din dayake hannunsa na goge Kai ya juyo ahankali cikin isa da wata irin izza ya nufo kofa ya fito. Aleey dayake palo a tsaye yana jiran fitowansa yana ganin fitowansa da towel take ya dauko sunglasses na Versace ya miqa masa hannu kadai ya saka ya karba yana nufar kofa Kai tsaye wadda tini aka wangale masa ita, Yana fitowa umbrella biyu a take aka bude take a kansa batareda ya tsaya ba suka biyosa dukkaninsu tamkar zasu fashe sbd karfi ga tattoos nasu daba wasu dake bayyane sai daukan ido sukeyi, Cikin mummunan tsoro da firgici bayin dake kofar bangaren sukai
🏠