7)MEENALLYN DADDY
Page 30 & 31
Bayan Na'ima ta gama karanta letter da Abdurrahim yabata dafa kanta tayi tana kuka sosai tana cewa" Wayyoo Allah na na ba ni wa zan ce ya yi min cikn nan Allah na rok'eka ka d'oramin cikiwan da zai zubar da cikin nan ba tare da na sha magani ba" Na'ima ta dad'e tana kuka har ta samu bacci b'arawo ya sace ta.
Washegari da wuri Na'ima ta ta shi ta tayi wanka kasan cewar yanzu saurin jin yunwa gareta yasa tafita ta ga ko hajiya Rahina ta ta shi in da da kan ta ta ke girkin ta bata da 'yar aiki, Na'ima ce ka d'ai wadda ke mata aiki ita ma kuma share-share ne kawai da wanke-wanke .Na'ima a kitchen ta hangi hajiya Rahina tana ta aikin had'a abin kari( breakfast) Na'ima har ta shiga kitchen d'in ta fito da sauri k'arnin k'wain da ta jiyo dan bata shiri da k'arni, tun kafin Na'ima tak'arasa shigowa hajiya Rahina ke kallan Na'ima ganin irin yadda ta yi k'iba tayi haske, bak'aramin mamaki hajiya Rahina ta yi ba ganin Na'ima tafasa shigowa ta koma tana dod'e hanci," Yarinyar nan lafiya kuwa?" Cewar hajiya Rahina, bayan hajiya Rahina ta kammala had'a kayan Karin ne ta Kira Na'ima ta bata nata. Na'ima tea d'in kawai ta d'auka tabar doyar.Na'ima d'auka ta yi zata shiga d'akin da yake mazaunin nata hajiya Rahina ta ce"zauna ki sha anan mana, nakira hajiya Suwaiba na ce mata ta turomin gwaggon ki Allah bashi sai ki fad'a mana halin da ki ka kasan ce bayan tunanin kin mutu da mu ka yi"Na'ima cikin sanyi ta ce" tom mommy ba damuwa Allah ya kawota lafiya"
Bayan Na'ima ta gama shan tea d'in da shi ka dai take iya sha, ta share falon ta goge duk wata k'ura da ke falon.Bayan ta gama ne ta na nan zaune gwaggo ta yi sallama ta shigo falon.Da gudu Na'ima ta ruga ta rungume gwoggo ta na kuka." laaa ka gamin shirman banza, me ye kuma na kuka ke da za ki yi farin cikin dawo da ki kai cikin danginki da Allah ya yi"Cewar gwaggon Na'ima. Hajiya Rahina ce ta fito jin shigowar gwoggo da tayi.Bayan sun gama gaggaisawa ne hajiya Rahina ta ce "dama gwaggo na kiraki ne dan ina so ko mai Na'ima zata ce game da b'atanta ta fad'a gabanki inda ni ke ce nasani amatsayin mahaifiyar Na'ima" Hajiya Rahina kallan Na'ima ta yi ta ce"Na'ima mun shi ga rud'u jin bacewarki kwata-kwata inda duk wa inda suka rasa ransu anga gawarsu, amma ke ba ki ba gawar ki, ina ki ka shiga Na'ima har tsawan watanni biyar ko shida? " Tun da hajiya Rahina ta fara magana gaban Na'ima ke fa'duwa, shiru Na'ima tayi dan tarasa ta inda zata fara.
"kin yi shiru Na'ima?" Cewar hajiya Rahina.
Na'ima cikin sanyi ta ce "Ni ma Wallahi ta ka mai-mai Ban san ya akai ba Wanda ya taimakan ya taimakeni,dan betab'a ban labarin ba ,abin da dai na sani bayan faruwar hatsarin Jirgin mu na farka na ganni agidan wani bawan Allah ba haushe ne kuma kuma musilmi anan naci gaba rayuwata na tsawan wata shida da na yi har Allah yasa ya biyamin kud'in Jirgi na dawo"Cewar Na'ima tana share hawayan dake zibar mata.
Hajiya Rahina kallan Na'ima tayi ta ce"takardar fa da na gani waya baki ita ?" Hajiya Rahina ta ciro letter da Abdurrahim ya ba Na'ima tana nunama Na'ima ita. Ita ko Hajiya Rahina ta ga takardar ne lokacin da ta shiga d'akin Na'ima ita kuma lokacin Na'imar bata ta shi daga bacci ba,anan taga takardar ta d'auka ta karanta.
Gaba d'aya Na'ima ta gama rud'ewa kuka ta fasa tana cewar"Wallahi gwaggo ba da yarda ta haka ta faru ba da..."Gwaggo tare Na'ima tayi dan ita basan me ya ke faruwa ba,ta kalli hajiya Rahina ta ce" wai hajiya mai me ke faruwa ne ,takarda me ye ne ki ka gani ?"
Shiru hajiya Rahina tayi dan tarasa ta inda zata fara yi ma gwaggo bayani ,sannan ta ce"tom gwaggo abi sa ga alama dai Na'ima da ciki ta dawo"Wata irin zabura gwaggo ta yi ta ce"Ke 'yar nan ki rufa min asiri ciki kuma! Kamar ya? " Na'ima ko ta dage kukan ta kawai ta ke yi.
Hajiya Rahina ta ce"tom Na'ima ta kuka kuma ai ta k'are in da aikin gama ya gama, amma taya haka ta faru Na'ima? Bayan kin san da aure kanki Na'ima!" Cikin kuka Na'ima ke cewa"Wallahi mommy f'yade ya yi min bada son raina ba ne"Daga hajiya Rahina har gwaggo shiru ka wai su kayi dan dukkansu sun rasa abin cewa, gwaggo ko kuka ta fasa tana cewa"Na'ima ya zanyi da mahaifiyarki? Me zance mata Na'ima? Da wa na ido zan kalleta?" Na'ima cikin kuka ta kuma cewa"Wallahi gwaggo ba da son raina b,,,,,,,,,,," Ke da Allah can yi min shiru yaza ai ki je ki zauna gida daga ke sai Namiji,wanda ba muharraminki ba ba d'an'uwanki ba ba dangi iya ba na baba balle ya kalliha" Cewar gwaggo.
Hajiya Rahina ta ce "Haba gwaggo tom ita da ba 'yar k'asa ba ina ta sani ai aikin gama yariga ya gama yanzu tashi zata yi mu je aima mahaifiyarta bayani"Gwaggo kai ta jinjina ta ce"Wallahi hajiya ba zan iya had'a ido da Mariya ba ince mata 'Yarta na d'auke da ciki, ina ba zan iya ba" Cewar gwaggo tana nai man tashi."ai hak'uri za ki yi gwaggo ta inda aka hau ta nan ake sauka dan haka dole da ke zamu ayi ma mahaifiyar yarinyar nan bayani"
Gwaggo ba dan ta so ba sai dan ba ta da yarda zata yi.Hak