masu gwaggo k'arin bayani suka fahimci duk abinda yafaru.
Kuka mahaifiyar Na'ima takeyi sosai tana fad'in "Allah sarki Na'ima ashe haduwar da mukayi itace ganawar mu tak'arshe"
Dukkansu Sunyi kukan su san rai dan bamai ba wani hak'uri, sai da mijin Hajiya Rahina ya dawo yayi masu nasiha akan shi komai da kuka gani muk'addarine daga Allah tunrar gini tunrar zane, nan dai alhaji yayi ta masu nasiha har Allah yasa jikinsu duka yayi sanyi bakamar maman Na'ima ba, saidai ita kad'ai tasan irin rad'adin da takeji acan k'asan zuciyar ta, Alhaji da kan shi yad'auki mama amotar sa shida Hajiya Rahina da gwaggo suka rakata har gida, bayan sun isa ne Alhaji yak'arayima ma mahaifiyar Na'ima nasiha sosai, sannan yaciro kud'i masu yawa yabata.
Kafin kace me mutuwar Na'ima takauraye duka sabon yalwa, koda labarin mutuwar ya isa kunnan dan gin baban ta, har gida su ka je sukacima mama mutumci sannan suka ce mata sunanan suna jiran dawowar Na'ima duk inda ta kaita," k'aryar banza in mutuwa ta yi dagaske kamar yadda ki ka ce ina gawar ta? " Cewar jimmai mahaifiyar gali Wanda aka d'aura auran sa da Na'ima.
Can b'angaran Na'ima ko tana ganin Abdurrahim yayi shigewar sa cikin gidansa ta na kuka ta fita daga gidan..........
🛥️ ABDURRAHIM🛥️
MATUK'IN JIRGIN RUWA NE.
🔔📚
*JARUMAI WRITER'S A SSOCIATION📚*
Na
Fadila Sani Bakori.
Wannan shafin gaba d'ayanshi na sadaukar da shi ga 'yar'uwata barrister Hassana Sani,Allah ya taimakeki yabada sa'ar jarabawa🙏🏻🙏🏻
Page 16 & 17.
Na'ima ko da ta fita daga gidan ja tai ta tsaya tana kuka dan bata san inda zata ba gashi duk inda zata waiga masu ja-ja yan kunne kawai take gani suma jefi-jefi turawa kenan.
Na'ima na nanan tsaye sai ga wani bak'in kare yana kewaye unguwar yana zaro harshe, duk dare Wannan karan shike gadin unguwar, Na'ima ganin karan nan na tunkarota yasa tafara ja da baya ganin karan da gaske gunta ya yo yasa ta juya ta shige gidan Abdurrahim da gudunta, tana shiga taja k'ofar ta rufe, amma duk da haka jikinta be dai na rawa ba dan ta matuk'ar tsorata da karan, cikin tsoro Na'ima ta samu can gefe agidan ta rakub'e tana mai addu'ar da duk tazo bakinta. Na'ima na nan zaune agun har wani wahalallan bacci ya kwasheta.
Can b'angaran Abdurrahim ko sai bayan ya shiga gida ya ke jin abin da yayi ma Na'ima bai kyauta ba dan dagagani yarinyar batasan inda zata ba, "Tom ai garama da yayi mata haka dan yarinyar tana bashi haushi gashi tak'i fad'a mai dalilin zuwanta garin "Tofa in ban da abin ka Abdurrahim ba sai ka tambaye ta zata fad'ama ba"inji wani tunanin nashi kenan.
Abdurrahim tunawa da yayi be rufe gida ba ne yasa ya tashi ya nufi wajan get d'in dan rufe gidan, torch light d'in wayarshi ya haska ya rufe gidan dan shi daga dare yayi Yake kashe hasken gidan.Bayan ya rufe gidan ne ya juyo sai ya ga abu kamar mutum ya k'udindine awaje d'aya kusan mutuk'an jirgin ruwa basu da tsoro k'arasawa wajan yayi amma abin mamaki Na'ima ya gani kwance agun ta k'udindine jikinta tana barci abun ta.
Bak'aramin tausai Na'ima ta ba Abdurrahim ba ji ya yi tausayinta gaba d'aya ya cika zuciyarshi.
Abdurrahim ya dad'e atsaye akan Na'ima sannan ya lallab'a yadda ba zata tashi ba ya d'akko ta kamar k'aramar baby ya yi cikin gidan da ita, d'akinta ya kwantar da ita ya ja blanket ya rufe ta sannan ya je d'akin shi shi ma ya kwanta.
Abin mamaki washegari Abdurrahim har ya yi abin da zaiyi na karyawa (breakfast) amma Na'ima bata tashi ba, har ya gama danne-dannan wayarshi ya je ya watsa ruwa,sannan jin shirun yayi yawa ya je ya k'ara dubata, still bata tashi ba, tunani ya farayi anya ko lafiya dan yau satinta uku ke nan agidan amma bata tab'a kai haka tana barci ba.
Abdurrahim shiryawa yayi ya fita gidan dan zuwa ganin yadda alheri ta kwana ya duba hannun ta da Na'ima ta ji mata ciwo kafin tai mai k'orafi.
Na'ima kamar jira ta ke Abdurrahim ya fita yana fita ta tashi, kallan d'akin ta farayi tana tunanin ya akai ta dawo nan,"Kai sai dai in dawo da ni akai" Na'ima ta dad'e tana tunanin yadda akai ta dawo d'akin amma bata samo ba, daga k'arshe tai tunanin k'ila bacci ne ya kwasheta shikuma da yazo rufe gida yatadata ta shigo, kai amma wani irin nauyin barci garan haka, tom amma in haka ne yayi min hak'uri ne inda yakoran daga gidan, nan dai takasa gano amsar ya yi mata ha'kuri ko kuwa daga k'arshe ta tashi ta shiga toilet tai wanka ta cire rigar Abdurrahim dake jikinta ta mai da tata data wanke, tom nan fa yunwa tace itama gatanan zuwa.
falon Na'ima ta koma, tananan zaune yunwa nak'aracinta Abdurrahim ya dawo gidan, Na'ima tashi tayi daga kwancen da take da sauri ta ce "Ina kwana" Lafiya ya jikinnaki ?"Abdurrahim ya fad'i maganar yana kallanta da kulawa." Na ji sauk'i sai dai,,,,,,,, "shiru Na'ima tayi takasa k'arasawa.
Abdurrahim kallan Na'ima yayi jin tayi shiru,kamar yayi banza ya rabu da ita sai kuma yaji bazai iya ba dan a