fad'a cikin tsantsar b'acin rai Na'ima ta ta shi rik'e da kunci ta ce"Bai war Allah mai ne miki zaki maran ko shima mairigar da ya ganni da ita ai bai cimin komai ba" Na mare ka dan ubanka" cewar alheri.
Na'ima ko cikin jin zafin zagin mahaifinta da akayi ta ce" ka da ki sake zagar min ubana yana kabari" Uban ka na ce na ce ubanka-ubanka" wani uban kukan kura Na'ima ta yi ta afka ma alheri, da ya ke alheri irin manyamanyan matan nan ce Wanda zaka gansu ga tsawo ga k'iba yasa ta rik'e Na'ima tai ta duka ,da taga abin bai ma ta ba shak'eta ta yi ta ce"Dan ubanka ya ka ke da Abdurrahim?"Ba dai ubana ba" cewar Na'ima.
Janta alheri ta ci gaba dayi ta ce"Inda bazaka fad'amin yadda kake da Abdurrahim ba, tom yanzun nan zakabar gidan nan dan ubanka" janta alheri tai ta yi har zuwa hanyar fita falon, Na'ima kuma sai cijewa take da d'an k'aramin k'arfin ta.Alheri ta ce"Dan ubanka gidan na ubanka ne Da bazaka fita ba? " ke ma gidan ai ba na ubanki ba ne"Ai alheri jin Na'ima ta zageta itama rud'ewa tayi tai ta bugun Na'ima tun k'arfin ta.
Abdurrahim ko yana can gidan alheri yana jiranta ta dawo, da ya ji shirun yayi yawa kiranta yayi awaya amma bata d'auka ba,rufe mata gidan ta ya yi Shikuma ya yo gida. Tun kafin ya gama parking motar sa yake jin hayaniya da saurinsa ya k'araso cikin gidan alheri ya iske tana tura Na'ima waje had'e da kai mata duka, tana sai ta fita inda gidan bana ubanta bane, ita kuma tana cijewa tana cewa bazata fita ba inda gidan banata ba ne.
Wata uwar tsawa Abdurrahim ya bugama alheri ya ce"Wa ya saki? " Alheri ko da ranta ya b'ace jin abin da Abdurrahim yace mata ta ce" Haka zaka cemin ko wayasani ,tom na rantse da d'unbun son da na ke ma yau sai ta b'ar gidan nan ,waya ce ma yasa ma ka riga" da ya ke haka take hausarta namiji ta mai dashi mace mace ta mai da ta namiji, itako Na'ima ta rakub'e gefe bak'inciki yasa sai kuka take yi, alheri kuma nuna Na'ima tayi da ke kuka ta ce"Kab'ar gidan nan nace" Allah sarki Na'ima ko kallanta batayi ba taci gaba da kukan ta, tun kud'ata alheri tayi tun karfinta Na'ima sai da ta bugu da get d'in dake gidan sannan tatafi taga-taga kamar zata fad'i wani k'arfe da ke kusa da Na'ima Na'ima ta d'auka ta yi kan alheri da shi alheri da taga bata da wani abu da zata kare kanta rugawa tayi sai dai duk inda tayi Na'ima binta take yi da gudunta ita ala dole sai ta bugamata alheri shi. ihu alheri ke yi Na'ima ko bata fasa bin ta ba. Abdurrahim da yaga indai ya kyalesu Na'ima zatai ma alheri rauni indai ta bugamata ,dai-dai ko Abdurrahim zai amse k'arfan Allah yaba Na'ima sa'a ta bugama alheri shi, dan ma Allah yasa ahannu ta same ta ba akai ba, wata uwar k'ara alheri ta yi ta zuk'unna agun tana rirrik'e hannun ta re da alkawarin sai taci uban Na'ima.
Da kyar Abdurrahim ya lallabi alheri ta tafi gida, ita kuma Na'ima tana ganin wucewar alheri ta kama hanya zata koma gidan hannu Abdurrahim yad'aga mata ya ce"Kar ki sa ke ki koma min gida" ya na kai wa nan ya shige ya b'arta agun.
Waiwaiye adon tafiya inji Hausawa,can kaduna ko gwaggo jerawa su kai da Mariya mahaifiyar Na'ima har'gidan da Na'ima take aiki kasan cewar me gadin ya gane gwaggo yasa ya barsu suka shiga kai tsaye, alokacin Hajiya Rahina tana waya da k'awarta Hajiya Suwaiba matar da gwaggo ke aiki a gidan ta,Hajiya Rahina ganin su gwaggo najiranta yasa ta katse wayar ta cema Hajiya suwaiba zata kirata anjima tayi bak'i ,sannan ta juya tana kallan su gwaggo ta ce " sannun ku da zuwa gwaggo" nan dai suka gama gaggaisawa, sannan gwaggo ta kalli Hajiya Rahina ta ce"Hajiya wannan da kike gani ita ce mahaifiyar Na'ima, na kawota ne in fad'amata yadda mukayi da Na'ima agabanki dan kar'ta zargan da cin amanar yarinyar ta" gwaggo ta ci gaba da cewa"Mariya bayan kin zo kinsanar da kina son Na'ima ta dawo gida sabo da auran da aka d'aura mata, tabbas agabanki Na'ima bata nuna komai ba, tom ammafa bayan kin tafi ga Hajiya nan itace sheda, Na'ima ta zauna sai rusamana kuka take tana rokan Hajiya akan dan Allah kasar da za'a d'akko ma Hajiya kaya za ai tafiyar dogon zango ta roki hajiya aje da ita wai kafin lokacin k'ila asamu mafita dan ita bazata auri mutumin da mahaifinta yabar wasiyar kar ta aura ba, hajiya tace ma Na'ima ita bazata d'auketa ba ta kai ta doguwar tafiya batare da amincewar ko wa na ta ba, sai dai ta fad'a ma mahaifiyar ta in ta amince, Mariya in tak'aicemiki magana Na'ima tazo tasamin kuka akan sai dai in amince aitafiyar da ita. Tom Allah yasani tausayin Na'ima yasani amincewa ,kin ji yadda akayi wallahi"
Kiran da akaima Hajiya Rahina ne awaya yahana mahaifiyar Na'ima magana, cikin furgici Hajiya Rahina ta tashi tsaye ta ce"Accident , kana nufin jirgin ruwan da ya d'akko kayan mu yayi accident?" Banji me akacemata ba daga can b'angaran naji tana cewa"Innalillahi'wa ina ilaihirraj'un, kana nufin ba aga Na'ima ba?" kashe wayar Hajiya Rahina tayi ta dafe kai tana karanto duk addu'ar da tazo bakinta.
Tun kafin Hajiya Rahina tayi