ragowar duk an salwantar
musu da rayuwarsu,idan ta haihu yaro baya cika shekara biyu yake
mutuwa, wadan nan biyun ne Allah ya tseran mata da su wato
Yarima Abbas da kuma gimbiya Jauhariya.
Sai mata ta uku wato HAULE ita ma kamar SIYAMAN ce
har ta fi Siya ma iya makirci da tuggu, matsalar ita bata taba haihuwa
ba, don haka ta koma ta kama kafa da Siyama, saboda SIYAMA duk
ta fi su dukiya, saboda danta ana ganin shi nemagajin Sarki duk wata
dukiya da za a bayar kyauta ga gidan Sarauta idan ta wuce Sarki to
shi ita ake bawa, ko a al'adance itace Shugaban gidan ta fuskar
fifikon Sarki,ta fuskar siye duk wani wadda yake da ruwa da tsaki a
cikin gidan biyayya take yi mata, haka duk wani da ke wajen gidan
da yake da alhakin kawo ma'aikatan gidan Sarauta to shi ma bauta
yake mata, saboda haka sai abin da ta ce a gidan ake yi.
A lokacin tana zaune a kan hamshakiyar kujerar mulki ta
cikin gidan Zuleha na gefanta a zaune barori da 'yan aikin gidan
Sarki na zagaye da ita, wasu mata na can wata da'ira ana busa da
gara garaya suna dan rausayawa, ta na zaune idon ta kyam akansu
tana murmushi, wasu in sun shigo sai sun je sun yi mata kamar sujjada su kuma sumbaci kafafuwanta sannan su nemi wajen zama su
zauna.
A wannan Lokaci Hauletu na bangarenta ‘yar ta yar kimanin goma sha biyar na gefanta a zaune da barori waje da cikin daki suna
masu jiran wata bukata a isar mata da shi, kaf cikin masu mata
bature
241Page
hidima Siyama ce ta kawo su, mace daya ce aminiya kuma 'yar uwa,
wacce ita ce kadai amintacciya a wajenta wato HINDU. Da ita take
duk wani sirrinta a gidan.
Hauletu ta dubi 'yar ta "ZAHRA ta ce "Ki je daki ki kwanta
za mu yi Magana da Hindu".
Zahra ta dubi mahaifiyarta cikin girmamawa ta ce mike tsaye
gami da jinjina wa "Na barki lafiya".
Ita ma Haulet ta jinjina kai ta ce "Sai na shigo duba ki a
turaka ki yi addu'a sosai ki kuma yi karatunki kafin ki kwanta".
Zahra ta fara tafiya ta na zuwa bakin kofa wasu mata biyu
masu yi mata hidima suka bi bayanta doguwar rig ace a jikinta an yi
mata dinki da na kawa rigar jikinta har jan kasa take yi kamar
Dawisu yana tafiya. Sai da ta fice aka mayar da kofa a ka rufe sannan
Haulet ta dubi Hindu ta ce "Yake 'yar amana ta, me kika sani
dangane da Kauyen Annur,shin kin taba zuwa ko kuma kina da
labara, ko akwai wani da kika sani a kauyen".
Da Hindu ta ji wannan batu sai ta yi shiru tana nazari cikin
dan lokaci ta dago da kanta ta dubi uwargidanta cikin nuna kulawa
sosai ta ce "Amincin Allah ya tabbata a gare ki, ‘yar malamai jikar
malamai, jinin malamai matar hamshakin Sarkin duniya Muhammad
farsi, ina da sani a game da kauyen Annur, har ma ina da alaka da
Hakimi Abdullahi bin Sharjas, ya sanni farin sani, domin tawagarsa
ce ta samo ni, ta kuma musuluntar dani, kafin ta kawo ni gidan
Sarauta, saboda haka na koyi abubuwan da yawa a cikin kwanaki
goma da nayi a gidansa kafin daga bisani a kawo mu nan". Haulet ta jinjina kai “Yayi kyau, na kuma godewa Allah da
na samu haka daga gare ki, abin da yasa nay i tunanin tambayarki a
game da birnin Kauyen Annur na taba ji kina maganar Kirkin
matarsa Kubra, a lokacin da kike bawa Hindu labarin jarumtar
bature
25 | Page
kauyen, ban kuma ta shi bukatuwa da son sanin ba sai yanzu da wani
dalili da ya ta so".
Hindu ta yi sunkuyar da kai domin jin daga bakinn Haulet, jin
shiru yasa ta ce "Ranki shi dade me kike nema daga gare ni, in sanar
dake dangane daga Kauyen Annur”.
Sarauniya Haulet ta yi shiru daga bisani ta ce "Wani abu ke
dauremin kai yake kuma sani tunani game da rayuwar kauyen, gashi
karamin kauye ne amma yadda kowane munafuki yake tsoron
kauyen abin yana daure min kai, hatta Sarki akwai shakkar Annur a
ransa akwai girmamawa ta musamman, a bangaren Sarauniya
Zulehat kuwa bata da wani tashin hankalida ya wuce ta ji an am baci
kauyen Annur, mahaifina in har ya zo wannan yankin to zai ce da ni
zai je Kauyen Annur ban taba tambayarsa wani abu da ke faruwa a
kauyen ba, sai yau na tashi da son jin labarin kauyen shi yasa kika ji
na fara da tambayarki, shin me yasa duk mai mutumci yake girmama
kauyen, me yasa duk munafuki yake shakkar Kauyen?"
Hindu ta yi shiru tana dan murmushi tana tuna wasu abubuwa
da suka faru a kauyen kafin ta dawo gidan Sarauta ta ce "Zama ne ya
kama mu a gidan a lokacin muna matsayin bayi. A lokacin da muka
isa Kauyen Annur a matsayinmu bayi mun taho cikin kaskanci da
yunwa kishirwa da wahala, amma kallo daya Hakimi Abdullahi bin
Sharjas yayi mana ya fuskanci damuwarmu a cikin Babbar Kasuwar
Birnin nan.
A lokacin ya kawo abinci da dabbobi daga kauyensa don
siyarwa ya same mu a kasuwa a cikin wannan halin mu biyar ne.
maganar farko da ya yiwa mafarautar mutane "Ku basu abinci da
ruwa su sha, idan kuka kyautata musu za su yi daraja maimakon ku
bar su suna cikin yunwa ga wahala".
bature
Daya daga cikin Dakarun ruwan sai ya ce "Ba z aka koya
mana yadda muke sana'ar mu ba, idan sun yi maka ka siye su ka
basu abincin da ruwa".
Bai j