tura abokina domin sanarwa Sarkin
garinmu cewar abiyo bayanmu saboda ga tawagar kafurai tare da
Keji waddaban yadda da shi ba ashekuwa wannan Keji dauke yake
daku. Nan da kauyenmu babu nisa, mu je na isar da ku wajen Sarki
domin a baku kulawa ta musamman'
"
Gimbiya ta ce "Mu na da nisa, sannan idan mun je kauyenku
tamkar mun kai muku jaraba ne domin dole sai an bibiyi sahunmu,
zuwa yanzu da ka tseratan da mu mun gode kabar mu mu shiga jeje
mu tafi can wani waje inda ba za a taba gano mu ba mu boya har mu
koma Kasarmu, ka sani cewa wannan tafiya da ake yi damu ita ce
tafiya ta karshe zuwa birnin nan don kai mu in da ake bukatar kai
mu,shi ne ka yi sa'ar dakatar da mu”.
Koda Jarumi Umar Bin Abdallah ya ji wannan zance daga
bakin gimbiya sai y ace da ita "Rayuwa kala biyu ce in ma a zauna a
bature
12 | Page
yi nazari mai kyau domin a samu a kubuta in ma a yi dirshan da
shawara mara kyau daga baya a yi danasani,zuwa fadar Abdalla tsira
ce daga gare ku, sannan Fadar Sarki Abdallah ba ta gudun Farmakin
abokan gaba, ba kuma ta juya baya daga ceton mai nema, idan haŋ
silar cetonku zai zame mana yaki, to za mu daura damara, idan kuma
sulhu ne za mu zauna a kujerar sulhu ya ke gimbiya kada ki yi jiji
dakai datakama ki biyo ni ba za ki tabe ba"
Da Gimbiya ta ji kalamansa sai ta samu yadda da abin da
yake fada mata amma a wata zuciyar sai ta ji wata kagawa ta zo mata
don me zai yi mata Magana a haka ba ladabi. Don haka sai ta yi niyar
kin daukar shawararsa. Duk da yayi gaba ya fara tafiya abinsa. Yar uwar tafiyarta wato Hadimarta HANZIYA ta dube ta ta ce "Ya ke
gimbiya kamar muna neman mu yi wa kanmu rashin adalci, a hakika
nin gaskiya muna neman dauki, ba don komai ba ko dan mu tsira da
rayuwarmu da kuma fadawa Koma Sarki Nasir kin sani sarai
matukar sun kai mu fadar Sarki Nasir duk wani takama da wani buri
naki ya kare babu wata mafita da ta wuce mu bi wannan sadauki”.
Gimbiya ta dube ta cikin alamun amsar shawarartada akasin
haka, daga bisani ta ce "Haka ne amma bakya ganin yadda yake
mana Gadara".
Hanziya ta yi murmushi “Ki manta da iko da takamamuna
halin neman ceton ne daga ubangiji kuma ya kawo mana wannan
Sadauki, lallai bujirewa wannan kamar rashin godiyar Allah ne".
Ba tare da ta kara cewa komai ba suka haye dawakai suka
nufi hanyar da ya bi suna biye da shi yana gaba a bisa Doki.
**
Birnin Bahara birnin albarka a wannan karni, kowane rai
yana fatan ya kasance a cikin birnin Bahara, saboda kasuwancin dake
gudana, sannan babu Kirista babu Arna, kowa yana iya rayuwa a
cikin birnin ya yi kasuwancinsa, sai dai bisa sharadi karya dokar
1
bature
1
28 Page
su kashe shi shi ne ya sa a wannan lokacin ba ni da wani sukuni tun
fara ciwo yau gobe lafiya gabana ki faduwa".
da Sarki yaHindu ta yi shiru cikin dan gajeren lokaci har sai da ta ji uwar
dakin nata ta share hawayen ta ja shessheka sannan ta ce "Neman
taimakon Hakimin Annur daidai ne a gare ki, domin shi mutum ne
adali kuma mai matukar son gaskiya, idan Allah zai baka kariya ba
da kansa zai zo ya baka kariya ba, amma shi ne zai zama sanadin
haka, kin fi ni sani duk wani ilimi a wajen kin a samo shi, tsantsaini
da tsoron fadawa halaka yake sawa kike wannan tunanin ai saka miki
damuwar da kuma tunanin nemo wadda zai tsayawa danki ki dauka
ubangiji ne yake haska miki, a da can ban da karfin gwiwa a game da
Yarima Abbas amma wannan maganar take ta sa na fara jin karfin
gwiwa, tabbas mu yi hanzari ka da mu yi kasa a gwiwa”.
"Maganar ki gaskiya ce, wannan haka yake, to amma yake
Hindu ya kike gani za mu yi wajen ganawa da Hakimi Abdullahi bin
SHarjasllah, ki sani cewar matukar sun san wani shiri to za su gyara
na su shirin, abin da nake tunani wani amintacce za ki nemo min
wadda zai kai masa ziyara wadda shi da kansa Hakimi zai nemi
yarima ni kuma zan gayawa yarima sakon da zai je masa da shi".
**
Lokacin da Jarumi Umar ya iso babban turakar mahaifinsa, a
daidai lokacin Hakimi na nazari game da bakuwar Suhaila bin
✓ Ababakari da kuma tunanin sakon da Sarauniya Hauletu ta zo masa
da shi na son haduwa da Yarima Abbas.
A wannan lokacin ya yanke kai ziyara babban birnin domin
ganawa ta musamman da Sarki a game da sabuwar masarautar da ake
rigima a kai, sannan kuma zai yi amfani da wannan dama ya gana da
Yarima Abbas.
bature
14 Page
Ya tsaya yana jiran umarni daga Waziri Jafar. Batare da Jafar
ya ba shi umarni ba ya mike tsaye cikin izza da isa sai da ya yi taku
biyu zuwa uku sannan ya dakata yana kallon Jarfis sannan ya ce “Ina
sokon da kake tafe da shi?"
Jarfis ya gyara tsayuwa ya ce "An taho da Gimbiya zuwa
wannan birnin zuwa dan takin lokaci yarana za su iso da ita kamar
yadda ka umarta za a kaita masaukin da ka umarci a a jiye ta a can”.
Waziri Ja'afar ya ce "Ka tabbata ka zabi kwararrun kuma
masana wajen aiwatar da wannan aikin kamar yadda muka yi da
Sarki Jarmusu Jakub".
Jarfis ya ce "Kamar yadda ya umarce mu haka komai ya
gudana, daga nan zuwa kowane lokaci dan