sanar da Kauyen kusa da su, daga nan ka wuce har babban birnin domin sanarwa da Sarki halin da muke ciki idan har ba a
kawo dauki ba Dakarun Mangalawa za su iya nasara akan mu”.
Yana gama fadin hakan dan aikin yayi sauri ya dauki doki ya sulale
ya bar garin, tuni guri ya yamutse da azababben yaki, babu ji babu gani ake
dauke ba dadi ya tsananta Hakimi tare da iyalansa da dakaru suna kokari
kare martabar garinsa, yayin da Jagoran dakaru na uku Barroji Ujjakallah,
da runduna ta bakwai Salkaf, duk a cikin tawagar da Bagulbasi ya taho da
ita daga yankin Mangalawa domin rushe musulunci a doron birnin Bahara
baki daya su mamaye birnin kamar yadda suka sha alwashi shekaru masu
yawa da suka shude.
Rundunar ta uku da ta bakwai runduna ce aka zabo manyan saboda
kowann Kwamandan yakinta jajurtacce ne kuma mai cikawa ne batare da
matsala ba, don haka Bagulbasi ya turo shi yankin nan domin ya shafe su,
ya zama shine misali na farko da za su fara aikatawa a birnin amma cikin
umarnin a taho masa da Hakimi Suleman Bin Ayyub saboda tsohowar
gabar dake tsakaninsu ta kin yadda da a yi sulhu a wancan shekaru sunan
bature
108
109 | Page
Suleman yana kan allon mangalawa saboda su ne suka so a mamaye su a kashe kowa a lokacin da suka kare a filin yaki dan haka dole sai an tara ire
irensu waje guda an gurfanar da su gaban Dodonsu kafin a shanye jininsu.
Batare dabata lokaci matansa barori da dakaru da duk wani mutum
yaro ko babba aka kashe shi cikin sa'a uku suka babbaki gari ko 'ina ya
zamana yana ci da wuta.ba tare da kakkautawa ba, abin bau tausayi dakarun
Mangalawa take gawarwaki suke yi suna shewa da murna cin nasara a karon farko.
Ba tare da bata lokaci ba suka dauki Hakimi Suleman suka daure
shi a jikin doki suka ja shi domin komawa masaukinsu, don gurfanar da shi wajen shugaban tawaga.
Sarki Muhammad Farsi na zaune a fada kamar kullum domin
‘ya'yansa ne za su gabato da irin kwazon da suka aikata a aiken da yayi musu sai ya zamana fada ta cika makil har a saman bene ta wata 'yar kofa Sarauniya Siyama na zaune tare da hadimanta suna kallon abin da ke faruwa a fadar Kamar kullum aka bude da addu'a sannan aka gabatar da Yarima Yazid yayi bayanin a game da aiken da aka yi masa zuwa Birnin Haiman, zuwa ga Benjamin, dukkanin abin da ya faru ya ci gaba da zayyanowa Sarki da wakilai na birnin da Hakimai tsoffin da manyan dattawan Sarauta suna kallo kuma suna saurarensa. Mahaifiyarsa gumi ne yake tsirfo mata domin ta san cewar lallai akwai damuwa duba da yanayin da take kallon fuskokin mazauna fadar Sarki musamman Dattawan fada. Sai da ya kare da yin bayaninsa tsaf mai rubutu yana rubutawa kamar a al'adance duk wani abu da aka zauna a fada ana tattaunawa z aka samu ana rubuta shi cikin wasu na’un fatoci falli falli.
**
Lokacin da Yazid ya gama jawabansa sai hankalin kowa ya koma kan Yarima Abbas a lokacin da ya fito ya tsaya ya fara karanto al'amarin da ya faru a birnin Shamnum da yadda ya gudanar da komai cikin nasara kuma aka zartar da hukuncin da ya dace, abin da ya rage ya barwa mai martaba Sarki Muhammad farsi don haka a cikin fadar duk wani mai kallon
mulkin birnin a matsayin tsira ne ga al'ummar duniya ba domin wani buri na tara dukiya ko burin son mulki ba sai fuskarsa ta cika da murmushi jin cewar lallai Sarki ya samu magaji, musamman dattawan birnin da Ulama'u wato Malamai magada annabawa.
Duk inda ran Siyama da na Waziri Ja'afar ya kai yayi mummunan faduwa, kuma zuciyarsu cike take da kuna da zafi mara misaltuwa. Sarki
ya bawa Yarima Abbas umarni da ya koma ya tsaya a matsayarsa. Domin *bature
3
110 | Page
ci wasu su zo su ci gaba da karanto al'amuran na yau da gobe abin da ya gaba da wakana kenan har ya zama an zo kan Sarki zai yi jawabinsa,
wadanda duk wani dake cikin wannan fada abin da yake so ya ji ke nan.
Sarki Farsi ya mike tsaye cikin juriya yana mai fuskantar jama'a ya
fara da cewa "Masarautar mu, ta wanzu cikin shekaru shekaru masu yawa
da kafuwa, an zubar da jini makiya Allah, wadanda 'yan uwa ne a gare mu,*
an zubar da jinin kafurai Mangalawa da sauran Bokaye 'yan tsibbu
wadanda suka saka birnin mu a gaba suna son ganin karshensa, cikin ikon
Allah da taimakonsa mun rusa birane mun kama birane mun musuluntar da
al'umma a ban kasa fiye da kima, mun yi aiki kafada da kafada wajen
jaddada Kalmar Allah.
Ina ba da tsohon labari ne da tun kafin zuwana duniya, zuwan
dukkanin wasu da suke nan duniya, mun jera da iyayenmu mun tari
bataliyar mayaka daga Rum, mun tare bataliyar mayaka daga hindi, mun
tare bataliyar mayaka daga sassa na duniya anyi hadin gambiza domin a
kawar da Daularmu, amma cikin ikon Allahu mun zamar musu gagara
badau. Ina daga cikin zababbun jarumi da sunansu ba zai taba gogewa ba a
doron kasa a can nahiyoyin kafurai da yahud domin irin nasarar da na samu
a kansu.
Na zama sarki saboda bunkasar jarumtaka ta, na zama zakara fidda
gwani a jerin dakarun birnin Bahara, zamowa ta Sarki labarin da bunkasa
ya ci gaba, amma lokaci ya wuce an fara sa