NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 4 of 42

dubi juna, uwar gidan tata ta jinjina mata kai alamar karfin gwiwa ita ma ta mayar da martani amma a cikin dar-dar. Har ta fita ta na kallon ta. Ta nufi wajen da zata samu ta tsirar da rayuwarta gadan-gadan majiya karfi na biye da ita aikuwa cikin sa'a sai ta fyalla da gudu bana wasa ba, su ma su ka bazama suna bin ta ta cikin ciyaye take suka zare Kwari da baka domin su harbe ta a kafada. bature 9 Page Dayan daga cikinsu ya sakankance cewar ya gama samunta sai kawai ji yayi ya yarda kwari dinsa kasa ga mashi nan ya huda hannunsa ya fito ta baya, ya kwala ihu, dayan bai san ta ina aka yi wannan harbin ba sai ya zare takobi yana jiran ganin ta inda maharbin zai fito, kwatsam bai yi aune ba ya gan shi a gaban wani katon sadauki mai suffer karfi Karo Jarumi Umar yayi masa da kai kawai ya baje kasa a sheme. Nan da nan ya bi bayan wannan budurwa inda ta diririce ta ma rasa hanyar da za ta bi. Kwatsam ta yi ido biyu da Jarumi Umar a gabanta kamar wani ifiritu Aljani. Abin duka take nema domin ta kwaci kanta ya ce "Kwantar da hankalinki, bana daya daga cikinsu, wadanda suka biyo bayan ki na kwantar dasu jinya suna neman agajin 'yan uwansu, tun dazu nake biye da ku”. Kafin ta yi Magana wasu masu, masu hatsarin gaske sun nufo in da yake da alamar dauke masa numfashi, kai tsaye ya zare takobi ya kifar da masu guda biyu zuwa gefe yayi a dingore zuwa ga budurwa ya fille kafafuwanta don ta samu zaman dirshan ka da kibiya ta same ta. "Kar ki motsa". Abin da kawai ta ji y ace ke nan sai ta neme shi ta rasa ashe waani tsalle ya sake yi ya fita da gudu kamar walkiya ji kawai ta yi mai harbin kibiyar yana ihu sai daga bisani ta ji karar karyewar kashinsa ɓass! Da sauri ya dawo gare ta "Ta shi mu je na kwabotar da ke suna da yawa, su iya cimmana". "Gimbiya" abin da ya ji ta faɗa ke nan". “Gimbiya” ya nanata gami da duban Keken dokin da kuma dakarun da suka durfafo shi "Bari na jarrabawa sa'a Da izinin Allah. Abin da ya furta ke nan ya zare takbobinsa ya tunkare su kai tsaye ba tare da tsoro ba Jarumi Umar yana ji da karfin jiki don haka ne a duk lokacin da zai kai wa mutum hari to sai ya saka jikinsa ya bature 10 Page bangaje a matakin farko kafin yayi amfani da takobi yan fara ɓasgar fuskarsa da ɓalla kasusuwansa, ta haka ya fara kafin daga bisani ya hau sara da suka da haka ya bazar da mutum goma kasa batare da sara ko suka ba, gadan-gadan yayi kan sauran sadaukan su ma suka® nufo shi cikin shiri ba tare da ɓata lokaci aka yamutse mutum ɗaya ya zamar musu kamar shaiɗan, ko wacce zuciya tunanin yadda za a magance matsalarsa ake yi addu'o'I su ke yi domin ganin yadda za su kwaci rayuwarsu daga hannun Jarumi Umar Bin Abdallah kafin ka ce mene ne wannan ya bazar da ragowar dakarun saura shugabansu da ke bisa doki yana zazzare ido da barazana “Idan ka so rayuwarka ta ci gaba da tafiya a doron kasa ka sallama idan kuma ka so ka bi sawun yaranka da suke kwance cikin jinya mu je zuwa" Duk in da jarumi yake yi baya ganin gazawa kullum gani yake zai iya domin a ganinsa shi ma za a iya tara masa dakaru sama da hamsin ya bazar da su, kamar yadda Jarumi Umar ya yi don haka sai ya kyalkyale da dariya ya ce “Kai Jarumin kauye masunci manomi kai gani kake wani abin bajinta ne domin ka salwantar da yarana, to maza bisa kanka". Ya rugo da gudu ya na ihu cikin salo ya fara kaiwa Jarumi Umar sara da suka, Jarumi Umar yana kare sara ya na mayar masa da kwarewa aka samu rabuwa ta martani shima yana karewa cikin dan lokaci kowa ya fuskanci lagon juna bai san waye Jarumi Umar ba shi yasa yake tsammanin zai zo masa da wannan salon ammaa lokacin da ya yiwa Jarumi Umar wata shiga sai Jarumi Umar yayi walankeluwa ya zille masaya wuce cikin iska fuu amma sai ya tangaje shi da kafada aikuwa wannan shugaban Barada yayi wata mummunan faduwa tamkar ya yi karo da dutse, tsoro da fargaba suka ziyarce shi a karon farko ya so ya saduda amma sai ya tuna shi ma Jarumi,cikin a zama ya mike tsaye ya fara neman takobinsa ya gyara mata riko ya kara dawo wani shammace Jarumi Umar yayi ya gabza baturė 11 Page masa naushi wanda yayi sanadiyar fitar hakoransa, yaransa da da suka samu ikon fardaduwa daga dakuwar da suka yi suka rirrike shugabansu. "Mai girma Jesus mu gudu wannan ba mutum ba ne". Ya na dagewa haka suka ja shi suka haye dawakai suka gudu Jarumi Umar yayi godiya ga ubangiji da ya bashi nasara ko da ya waiga inda budurwa take ashe tuni ta kwance yar uwarta daga cikin Keji ta kuma fito da ita. A hankali ya kara so inda suke su biyu suna kallonsa su kansu sun tsora ta da lamarinsa Gimbiyar ce ta ce "Waye kai? Ka sayar da rayuwarka a kan ceton ta mu alhalin baka san mu ba,mene ne bukatarka?" Maganar ta cikin izza ta masarauta, haka akwai tunkaho da isa a ciki, wato dole sai don wata bukata za a taimake su. "Ni suna na Jarumi Umar, daga kauyenmu zuwa in da na hange ku babu nisa, na saka ido ne a kan tawagar ku saboda tunanin akwai wani abu da aka boye na
🏠