NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 38 of 42

shinmu ni da kai ya bushe sannan burinmu a kan Yarima Yazid bazai taba yiwuwa ba, abu na biyu kuma yanzu haka Sarki ya fara zargin akwai wani kulli da aka yi masa amfani da shi dan dauke hankali a kan mulkinsa da yake yi kasalada gajiyawa da rashin maida hankali da aka yiwa kwakwalwarsa aiki, ya fara tunanin neman magani don ya ce dani zai nemi magani har ma a jiyan ya fita da yammaci na sa abin bayansa bai tsaya ko ina ba sai gidan Shuhul Islam, bayan nan kuma suka zaga gari suka dawo gida, yanzu ya kai Waziri Ja'afar mene ne abin da kake ganin za mu yi domin magancematsalolin nan da za su saka mu asarar duk tanadinmu?" Waziri Ja'afar yayi a jiyar zuciya gami da cewa “Ranki ya dade akwai babbar barazana da matsaloli da sai mun yi da gaske za mu iya kawo karshensu, abu na farko shi ne rashin kwarewa ne muraran yarima ya aikata wajen fito na fito da Benjamin, abu na biyu kuma ba mu isa mu hana Sarki neman magani ba, idan har muka ci gaba da hanawa ko Magana da likitocinsa ba kowane likita bane zai ji shakka ko tsoronmu kamar yadda na baya suka yi, ba ma musan a ina zai samu likitan ba bare mu yi tunanin wasu dabarun tsoratarwa ko zuba dukiya don hana aikin na bature 105 | Page hakika, a shawarce mu ja da baya, matukar ba so muke mu kwana kiyama ba, mu taya Sarki neman magani idan ya so daga baya sai mu sake sabon shiri". Tun da ya fara Magana zufa take keto mata domin ta san dama zai iya biyowa ta wannan bangaren domin shi kansa ta siye shi ne ta dalilin zai ci gaba da zamaa matsayinsa na waziri matukar in Sarki ya mutu danta ya zama Sarki, tana amfani da shi ne saboda soyayyarsa da mulki da kuma kudi, da mugun kishin da yake da shi ga duk wadda yaga ya fishi kusanci da Sarki, sannan ta sa Sarki ya yafe masa kurakure masu yawa. "Kana ganin idan Sarki ya dawo hayyacinsa, zai ci gaba da zama da kai amatsayin wazirinsa bayan akwai korafe korafe akanka da dama,, ka da ka manta badakalar kasuwa, masarautar Shamnumda hadakar da kake yi da kafurai". Ya dube ta cike da mamaki, ya san ta san yana da alaka da shamnum da wasu korafe korafe amma bai san ta san badakalar da yake yi a kasuwa ba, da kuma hadaka da yake da su da kafurai. Nan take hankalinsa ya tashi ya bude baki zai musa mata "Waziri Ja'afar babu wani taku da kake yi a cikin masarautar Bahara da ban san da it aba, na zabeka ne saboda na san za cika min burina na ganin mun gaji sarautar bahara daula ta dawo hannun dana, idan har ka ce zaka juyamin baya kwana biyu uku kacal yayi yawa kanka zai rabu da gangarjikinka domin kalma daya tak na sanar da sarki na kafa shaidun na gaskiya kashinka zai bushe, ka ci gaba da amsarumarni daga wajena mu gudu tare mu tsira tare”. Ya saka babbar rigarsa ya share gumin da yake tsattsafowa daga jikinsa hankalinsa ya kara ta shi y ace "Ranki ya dade wane ni na juya miki baya, baki fahimce ni ba ne...." "Na fahimceka, tunda za ka ci gaba da zama da Sarki a matsayin waziri baka da damuwa, za ka koma kalallaba Yarima Abbas ka dinga yi masa biyayya domin ganin cewar ya taka matsayin zama Sarki daga nan shikenan ka tafi kabarmu duk ukubar da ta zo kan mu za ta afka, idan har ka yi ganganci to la shakka kwana uku kacal mutuwa za ta yi maka sallama". Ta na fadin hakan ta mike daga inda take bata kara saurarensa ba ta wuce cikin gida, jikinsa a sanyaye haka ya mike lallai mata shaidanu ne na gasken-gaske zikirin shaidancin matan nan da su ya isa fada kwata-kwata jikinsa babu kwari. bature Tun a daren jiya da Jarumi Umar ya dawo daga fafatawa da Mangalawa ya zamana cewar cikin kauyen Nur suke cikin shirin domin suna da tabbacin matukar sun fahimci daya ne daga cikin kauyan ya yake. su,to babu shakka za su biyo sahu, don haka tun daga farkon shigowa garin aka kara masu tsaro da masu kai rahoton farmaki, saboda kasancewar cikin shiri. Lokacin da Umar suka kadaita da mahaifinsa sai ya ce "Ya Abbana, ka yi sani cewar zan iya ja da bataliyar Mangalawa guda ni da abokaina, akwai yara kanana da mata a cikin birnin nan, saboda haka zama na a tare da ku akwai babban hatsari, musamman in sun gano cewar ni din danka ne, zai fi kyau da muhimmanci na fita daga garin nan na nausa wani wajen yadda za su biyo bayana..." Abdullahi ya jinjina kai game da duban dan nasa ya ce "Ya kai dana, shin baka yi sani cewar rayuwa kashi biyu ta kasu ba, rayuwa ko mutuwa, Mangalawa sun iso cikin yankin Bahara da mayaka runduna runduna, wannan alama ce ta gagarumin yaki ya tunkaro kasar Bahara, sulhu da Mangalawa ba zai taba zama alkairi ba, domin idan har Mangalawa sun nemi a yi sulhu wahala suka sha kuma sun nemi sulhu ne domin a kyale su su je su kara shiri. Allahi ya ji kan Sadauki Nabaru, a waccan lokaci tarihi ya nuna cewar kada a bar kowane Bamangale a doron kasa, matukar bai yi imani da ubangiji musulunci ba domin ba za su taba saduda ba, a lokacin da yaki ya ci su aka kashe sama da kaso takwas cikin goma na mayakansu, sai suka yadda da a zauna a yi sulhu, wadda a wannan lokac
🏠