ba?"
bature
102 | Page
Nan take Shehul Islam da Sarki suka kara nutsuwa domin jin
amsar da wannan mutumin zai bayar sai ya ce "Ilimi kogi ne dan
samari, ni ma a nawa bangaren ina da ja akan maganar malam
Albardi to amma da nayi zurfin ilimi nayi bincike sai na gano cewar
akwai litattafai na addinin Islama da aka kifar a ruwa aka salwantas
menene dalili kifarda su, mene ne dalilin da yasa aka salwantar da su,
dalilili yana kan litattafan malam albardi wadanda nan gaba kadan za
su ke yawo a tsakaninku, da kanku za ku cimma wannan hujja”. Mutane suka fara maganganu a junansu har Malam yayi
musu sallama haye Rakuminsa gami da tafiya yana mai yi musu
murmushi cikin salama
Sarki ya dubi Shehul Islam yace "Ya kake ganin za a yi da
wannan kafirin?"
Shehul Islam yace "Idan muka daure shi ko kama shi wani
zai zo ya fara wa'azin cewar saboda zai fadi gaskiya an boye shi ko an kashe shi, abin da ya za mu yi yanzu mu baza idanunmu a duk
inda za a yi wa'azi mu kirawo wadannan mutane domin zama dasu, a
bainan nasi mu kunyata su mu karyata su da ilimi ba ta kaifin takobi
ba, muna saka takobi a cikin wannan lamarin komaiya lalace".
Koda Sarki Muhammad Farsi ya ji wannan batu sai ya jinjina
kai ya kuma yi amanna da shehil Islam daga haka sukaci gaba dazagaye gari har zuwa daf da magriba adaidai kofar wani gida suka tsaya suna son su samu ruwan da za su yi alwala su yi sallah domin
kada lokaci ya kufce musu.
Suna nan tsaye suna tunanin abin da za su yi gida ne gua daya tal a wajen daga haka sai filaye Shehul Islam ganin hayaki yana
tasowa daga cikin gidan ya ce "Da alama akwai mutane a cikin gidan nan don haka bari mu nemi su taimaka mana da ruwa domin mu yi
alwala. Kafin ya ji ta cewar Sarki ya kwala sallama aka amsa masa
dakyar daga jin murya tsoho ne ko tsohuwa.
Suna nan tsaye suna jiran a leko sai ga tsohuwa tana takowa
da sanda dakyar ta kara so gare su "Ku ne kuke sallama?"
Suka amsa "Sannunki"
Ta amsa "Yawwa, wa kuke nema?”
bature
103 | Page
"Shehul Islam ya ce "Muna neman ruwa ne domin sallah ta
riskemu a halin tafiya”.
"Sallah za ku yi?"
Shehul islam ya amsa da cewar "Sallah za mu yi, ko akwai
masallaci nan kusa?"
"A'a babu masallaci, yanzu masu arziki sun rabu da gina
masallaci, masarautu ma sun rabu da ginin masallaci sai gidajen
rawa, gidajen bakin haure ma'abota littafi, daga nan tafiyar da za ku
yi ku riski masallaci har sai kun danganta da cikin gari sosai".
Sarki Muhammad Farsi ya ji kamar ta soka masa kibiya a
cikin kokon zuciya, yaushe rabonsa da gina masallaci, a kullum da
kodayaushe gini ake yin a bakikamaryadda ta fada".
Su ka hada ido da SHehul Islam ya tuna lokacin da Shehul
Islam ya ziyarce shi Idan aka ci gaba a haka ya Sarkin duniya za mu
tsinci kanmu a koma baya sosai, mun bar gina Abubuwan ci gaban
musulunci mun zauna muna gina rayuwar baki, ban ce baki kada a
basu masauki ba, amma hakan kada ya dakatar da mu aikata abin da
zai bawa addininmu ci gaban, makarantu don koyar da al'umma,
masallatai don samun wadatar bautar Allah"
Dukkaninsu sai da suka tuna wannan maganar a tare suka
sauke ajiyar zuciya Sarki Muhammad Farsi ya dubi Shehul Islam a
lokacin matar ta koma domin daukar musu ruwan alwala "Matukar
Daular Musulunci ta fadi ni ne alhakin komai, domin ire irenku kun
yi min bayanin da ya dace nayi dogon tunani da nazari amma hakan
ya gagare ni, tabbas na cancanci tuhuma, na kuma amshe laifukana".
Shehul islam bai ce da shi ko ta tafasa ba saboda a lokacin
tsohuwar nan ta zomusu da ruwa suka yi alwala suka gabatar da
sallah sannan suka ci gaba da tafiya **
Tun lokacin da Waziri Ja'afarya ji sakon da Sarauniya ta aiko masa da shi hankalinsa yayi mummunan tashi ko baccin kirki bai iya
yi ba, haka washe gari ya kago rana ta raba domin ya samu isa wajen
Sarauniya domin su tattauna abin da yake akwai aikuwa lokaci na isa
bai tsaya bata wani dogon lokaci ba ya haye dokinsa sai gidan Sarki
bature
104 | Page
Muhammad Farsi. Yana isa kamar yadda yake cewar ya kagauta
lokacin nan yayi ita ma sarauniya Siyamata saka hadimanta mafi
kusanci da ita cewar a duk lokacin da waziri ya iso su sanar mata
domin ta gaggauta fitowa dakin gani, aikuwa yana bargar ajiyar
dawakai sai ga wani cikin masu yiwa Sarauniya hidima daga wajer
gidan Sarki ya zo ga Waziri ya sanar da shi cewar yayi maza ya isa
dakin gani tana saurarensa a can.
J
Batare da bata lokaci ba ya isa wannan guri. Babu wani
dogon bayani ko gaisuwa ta dubi Waziri Ja'afar ta ce "Muna cikin
babbar matsala da musifa abu biyu ya faru a lokaci guda wadanda
dukkaninsa asara ce mu a wajenmu, Yarima Yazid yayi mummunan
kuskure inda ya je ya fafata da Benjamin harma sun yiwa juna rauni,
labara ya zo mana cewar Yarima Abbas ya isa birnin Shamnum ya
kuma gyara dukkanin matsalolin da muka kunna a cikin birnin abin
tashin hankali ace Sarki ya gano muna da hannu wajen zuga Waziri
Ja'afarda mahaifiyar yarima Hilal, idan har Sarki Muhammad ya ji
wannan a lokacin da ya nemo lafiyarsa ka