NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 36 of 42

yake dan wane kauye ne". Ya na gama fadin haka wani mutum biyar daga cikinsu suka fadi gabansa "Za mu cika umarninka ya kai shugaba Ulgut,da iznini wuta mafi girman daraja”. Daga fadin haka kawai sai suka mike suka sauya kamanin suka haye dawakansu suna tafe suna bin sawayen dokin Umar. ** Lokacin da Sarki Muhammad da Shehul Islam suka ajiye dawakansu suka nufi inda majalisar dattawan nan suke in da suke tattauna al'amuran rayuwa sai Sarki Muhammad da Shehul islam suka tsaya daga nesa kadan kamar suna jiran waani har ya zamana wadanan mutane basu lura da su ba domin hirar da suke yi ta dauke musu hankali daya daga cikinsu yana Magana suna saurarensa dattijo ne mai kimanin shekaru hamsin yake baya ni "Daular Dut ta ruguje ne dalilin auratayya da Sarki Shamnar yayi, bayan ya bijirewa yan uwansa ya aure bayahudiya a hankali ta dinga jawo 'yan uwanta cikin masarauta har ya zmana Yahudawa sun yi tasiri a cikin sarautar DaularDut suka dinga aiwatar da komai babu wadda ake jin bature P 99 maganarsa face ya hudu batare da kowa ya san yahudawan bane, kuma a karshe majiya ta zo matarsa da ya auro ce take samar da su a cikin birnin ta karkashin kasa tare da sahalewar wasu mutane a cikin daular. To ina mai tabbatar maka cewa sarautar Bahara idan has Sarki Muhammad bai tashi tsaye ba, abin da ya faru a wancan daular tabbas za ta iya faruwa a nan, duba da yanayin da kasar mu ke ciki yanzu,ka duba fa ka ga, yadda dansa ne yayi tattaki zuwa birnin shamnur ya samar da adalci ga 'yan uwan juna ya kafa mulki ya yaki adalci ya kori tsinanne Waziri Adnan, shi yana kwance a gida banda Hakimi ABdallah ya ziyarce shi da bai san da wutar da ake tonawa ba". Sarki da Shehul Islam suka dubi juna cikin mamaki da taʼajjibin yadda maganar ta yadu a kankanin lokaci. Jin za su ci gaba da katobara Shehul Islam ya ce "Ranka ya dade mu je gaba❞ Har sun fara tafiya wani daga cikinsu yake cewa "Ba ma wannan ba, yanzu ka duba fa ka ga, yawancin Kauyukanmu sun daina shigowa da samarinsu zuwa kasuwancin babban birni tunda ana shan giya, ana caca, ana yin duk wani nau’in zunubi har gidan mata masu zaman kansu akwai a boye a cikin birnin mai tsarki kamar Bahara da shekaru da dama bayin Allah suka samar masa da nutsuwa lokaci guda mutum daya ya ruguza mulki shi yasa Mahaifiyata ta taba cewa da ni "Isma'il Farsi shi ne ya dace da mulkin Bahara amma aka batar da shi aka wulakanta shi a wata majiyar ma ana tunani sun haukatar da shi." Hankalin Sarki Muhammad farsi yayi mummunan tashi a lokacin da aka tuna masa da dan uwansa Isma'il batare da SHehul Islam fara tafiya ba shi ya fara tattaki ya bar wajen. karkashin Idan mulki al'amura munana sun rincabe a mulkinka ka kasa gano mafit, ka yi badda kama ka sulale ka shiga cikin al'umma batare da sanin ko kai waye ba, domin duk lokacin da mulkinka yake kan doron zalunci ba zaka yi nisan kiwo ba za ga bature 100 Page 101 Page fuskanci matsaolinka, idan kuma mulkinka na tafiya daidai akan gadon baccinka ma zaka iya fahimtal Wannan tunanin ya fado masa a rai a lokaci guda, lallai yayi sakaci mai girma. Tsakiyar gari suka nufa suka ga cincirindon mutane sun kewaye wani farin mutum mai cikar kamala da haiba, yana sanye da tufafi farare tas, da rawani a kansa baki, kayansa har zuwa idon sahunsa na kafa, da kyakkyawan murmushi a kan fuskarsa yana bayani dalla-dallah. Basu zame ko ina ba sai a wannan wajen. "Tabbas bayan annabi Muhammadu, babu wani annabi da zai kara bayyana, kur'ani ya tabbatar mana da wannan shi ne annabin karshen kamar yadda kur'ani ya tabbatar mana da cewar Annabi Adam shi ne annabin farko. To amma fa ba ana nufin shi kenan bayin Allah sun kare ba, shi kenan Allah ba zai kara turo wani ba, bayan manzo, akwai mutane halittu da suke zuwa duniya da karamomi su ma duk daga Allah suke, sannan akwai na'u'ikan mutane masu daraja da suke zuwar da sababbin abubuwa wadda Allah yayi musu baiwar da Ihlama Allah yana sanar da su, ta fanno ni da dama yadda za su gyara waal'umma ibada, bayan wafatin ma'aiki an samu sahabai da suka gyara wasu al'amura na addini, jama'a da dama suna karyata Shehun malami Albardi Ibn Ru'uyan wadda yau shekaru dari uku da rasuwarsa wadda ya zo da tabbatuwar auren wadda ya bi addinin kiristanci ba daidai yake da wadda ya zauna babu addini ba, ya tabbatar da kirista zai shiga aljanna kamar yadda musulmi wadanda suka yi zunubi za su shiga aljanna illa dole sai an saka su a wuta an an yi musu hukuncin da ya dace da su”. Sarki Da shehul Islamsuka kalli juna gami da cewa "Auzubillahi minalshaidanir raj'em" har Sarki zai motsa sai Shehul Islam ya ce "Dakata ranka ya dade, idan har mun dauki mataki anan dukka damarmakin da ya dace za mu rasa su, muna bukatar sanin su waye su, daga ina suke? Mene ne ilimin da suke son isarwa.... Wani nutsattsen matashi ya ce "Malaman addinin musulunci da suka gabata sun tabbatar mana da cewar duk wadda ya hada wani da Allah kafiri ne, kuma kafiri ba zai taba shiga aljanna
🏠