suna tafiya suna tattaunawa a cikin tafiyarsu ne aka zo wani majalisi inda wasu dattawa suke zaune suna hirarrakin yau da gobe da alamun makotan juna ne, Sai Shehul Islam
ya ce "Mu ziyarci wancan majalisi ko za mu iski wani labarin
sarautar birnin daga gare su
**
Lokacin da Umar bin Abdallah ya fito daga cikin gida domin
yin shirinsa na fita zagayen jeji kamar yadda suka saba shi da
abokansa a kowacce yammaci suna zuwa Jeji su yi karamar farautar
abin da za su zo da dare su gasa a naman da suka samo, suna gasawa
suna ci suna hirarsu cikin aminci da kaunar junansu.
Koda ya fito Shema'u na gefe guda tana kallonsa, har ya isa
bargar dawakai ya kwance dokinsa ya jawoshi izuwa farfajiyar tsakar
gidan. Ya saka masa siddi yana shafa gashin dokin, kamar ance daga
kanka ya daga kai domin duba turakar da aka sauke su gimbiya
Suhaila, dafda lokacin ta fito daga cikin turakar suka yi ido biyu sun
dan jima suna kallon juna. Kunya ta kamata a lokacin da ta dawo
hayyacinta ba, ta yi gyaran murya gami da karasowa inda yake.
Shema'u tana tsaye wani haushi ya kamata ta ji kamar ta je ta shake
ta ta mutu, dole sai ta yi maganin wannan yarinya dole ta fada cikin
ranta.
Gimbiya Suhaila ta kara so dauke da murmushi da kuma
kunya rungume a fuskarta, kyakkyawa ce Suhaila a fagen kyawu,
tana da zati da haiba matuka gaya tana shafa bayan dokin “Jarumi ina
kake shirin tafiya?"
bature
2
95 Page
Ya tsaya da shafa wuyan dokin cikin murmushi ya ce "Yar
Sarki zan tafita farauta ne ni da abokaina?"
Ta daga idanuwanta dara dara kamarmadara farare sol ta kara
da tattausan murmushi "Farauta a wannan lokacin?"
Ya ji wani abu ya soke shi a cikin ransa hankalin kwance ya
ji yana rage shakkarta domin yana ji a ransa akwai wani abu dangane
da ita "Muna zuwa farautar yammaci domin samar da abin zai ta ya
mu zama a daren da zai gabata".
"Uhmm"
Ta daina shafa dokin ta rike hannuwanta guda biyu waje guda
"Yaushe ka huta daga doguwar tafiya da har zaka fita, farauta kar
kamanta tafiya sa'a biyar ka shafe a hanya zuwa nan me zaihana ku
hakura ku huta, hutu yana da dangantaka da samun karfin gobe”.
Ya yi murmushi "Na so haka, to amma shi ma yawaita motsi
yana kara samar da horarwa a kowane irin hali, ban sani ba ko
abokan tafiya ta za su iya biyo don ban sani ba”.
Tana tunanin wani abu a ranta amma babu lokacin nazari ta ji
bakinta yana fadin abin da ke ranta "Dama za su ki zuwa su barka
kai kadai".
hakan".
Murmushi yayi "Idan basu je ba ke zaki yi min rakiya?"
Ya fada cikin karfin gwiwa domin yana tunanin tana bukatar
Ta kara fadada murmushinta "Zan so na fita farauta domin na
kara ganin salonka".
Murmushi ya kara yi ya mika mata linzamin dokin don ta rike
ya nufi bargar dawakai da murmushi a ransa ya jawo wani
kyakkyawan farin doki ya ce "Batare da na ta kura sub a mu je nay o
mana farautar?"
Murmushi kawai ta yi ta kama dokin ta haye, shima ya haye
nasa dokin suka jera Kubrat na daga cikin babbar turaka tana
bature
kallonsu, murmushi ta yi kawai ta jinjina lamarin domin ta gama
karantar yanayin.
Tun daga farfajiyar gida suka fara tafiya sai da suka fita cikin
gari sannan ne ta zaburi dokinta domin ta jangwalo shi su yi tsere
yanayin yadda ta hau kan dokin tun a fari ya fahimci kwarewarta da
iya sukuwa, don haka bai yi mamaki ba domin duk ma'abocin doki
mafi kwarewa ya samu fili to zai sake shi ne, bai gama murmushi ba
shi ma ya rufa mata baya. Gudu suke suna kara dawakai kwari
gwiwa suna tsale da shillo.
Da wasa ya dauki abin har suka isa inda nan ne za su dakata
amma bata tsaya ba yana mata alama da ta tsaya domin an zo gejin
da tsallaka shi zai iya zama matsala amma bata fahimci abin da yake
nufi ba, ya karawa dokin kaimi a karon farko ya tisa ta a gaba,daf da
zai isa inda take ya hango wata rundunar mayaka marasa iyaka sun
yanyame ko'ina tana waigensa bata Ankara ba tana kara tunkarar
wadannan mayakan, batare da ya dakata baya ci gaba da zaburar
dokinsa don ya hanata isa wannan wajen ya zamana bai fi kiris ya
rage ta isagare su ta juya ta cigaba da kallon gabanta sai idon ta yayi
tozali da dakaru sun tsaitsaye suna kallonsa har ma wani dake
gabansu ya amshi kibiya ya saita ta yana shirin harbota. Umar yayi wata kabbara dokinsa ya shakan nata dokin ya ja hannunta don ta yi
gefe aikuwa tana kaucewa kibiyar ta wuce fuu!. Ya sake hannunta ya
ce da ita "Juya"
A tare suka juya dawakansu suka kara zaburarsu a fusace
"Zaki iya ko na dawo da ke nan?”
Cikin nuna jarumta ta amsa "Mu je zuwa".
Shugaban dakarun Mangalawa Sashin ULGUT ya dakawa
wasu dakaru goma tsawa "Ku zo min da su".
Nan take suka su ka bi bayansu a tsiyace gudu na kece raini
aka dauka ana fafatawa ga harbi da suke yi da kibiya da jifa da
mashi, hakan yasa zuciyar Umar ta karaya domin yana ganin
Gimbiya Suhaila zata iya sarewa don haka ya ce da "Ki yi maza ki
bature
96 Page
97 Page
karasa gida abokaina ki sanar da su cewar ina cikin halin fada da
Mangalawa lallai su kawo dauki kafin su cin min?