NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 33 of 42

da yake bata karatu sai ya tunkari cikin dakin karatun. Yana zaune a durksuhe da dalibai a gabansa sun tsirawa guri guda ido inda yake musu bayanin game da addini, kai tsaye ya samu wajen ya zauna a ka zagaye malam da shi batare da kowa ya fahimci wane ne ba" "Ilimi wajebi ne ga musulmi, domin da ilimi kadai ne zaka fahimci wane ne addininka wane ne mahaliccinka, sannan zaka fahimci wanene shugaban halitta, idan hark a bar kanka babu ilimi lokaci zai zo da za a yi ta sabawa koyarwar ma'aiki domin kawo rudu daga cikin addininmu, ga ka musulmi a riga amma kafuri a zuciya, abin da zai kawo maka kariya daga wannan gubar ka san Allah kuma ka san Manzanninsa, Annabi Isa (Alaihil salam) bawan Allah ne, kuma manzon sa ne, wadda Allah ya turo domin isar da sakonsa, ya isar sun kashe shi, daga bisani an sauya labarin me ya faru, shine suke bautawa a matsayin Allah, wannan aikin shirka ne, darasi ne a gare mu, da muka zamo a cikin al'ummar Annabi mafi girman daraja a wajen Allah, akwai mushirikai da suka juya wancan lamarin ya koma Allah, ba za su yi kasa a gwiwa ba za su yi ta kafa siradi har duniya ta nade ba za su fasa ba, za su dinga danganta Allah da Annabinsa, wasu za su yi kokarin canza labarin to amma ilimi bature kadai ne zai zame mana mafi amfani a rayuwarmu da ta al'ummar nan gaba". A nan ne malam ya dago kai yana duban dalibansa ya zurawa mutumin da ya zauna ido bai ganeshi ba har sai da ya dago kai sukayi ido biyu da Sarki Muhammad Sarki Muhammad ya yiwa SHehul Islam alamun yayi shiru ya ci gaba. Wani daga cikin dalibai ya ce "Ya shehul Islam an ce Ka bautawa Allah shi kadai ka roke shi biyan dukkanin bukata ba za iya rokon Annabin Allah ba kenan?” “Shehul islam yayi murmushi ya ce "Allah da bakinsa ya furta cewa (Ihdinalsiradalmustakin) babu wani wadda za ka roka biyan bukata face Allah babu wani da zaka bautawa face Allah, shirka ce ka hada Allah da wani. An je ma'aikin Allah yana fushi da hani akan hakan, ya shaida mana cewa shi manzon Allah ne wato dan aikin Allah ne, Allah mabuwayi yayi bayani a al'kur'ani game da zuwan Annabi Muhammad,ya gaya mana fifikonsa da sauran Annabawa, shi ne Annabi mafi daraja yi masa karya, kafirci ne, bare kuma ka bauta masa ko ka hada shi da Allah". Wannan mutumin yayi shiru ya ce "Malam ni daga Dusara nake tafe yau kwana nan arba'in a Birnin Bahara, kuma ina yawaita zuwa karatunka, duk inda na ji ana wa’azi na kan tsaya na saurara, na ci karo da wani malami a dusara yana mai fadin “Idan har baka hada rokon Allah da sunayen Annabi ba, to addu'arka ba za ta taba karbuwa ba?" Malam ya dube shi ya ce "Kamar yaya?" "Ya ce Sai dole Annabi Muhammad (SAW) ya amsa sannan Allah zai amsa." " ?" Malam ya furta kai tsaye ya ci gaba da cewa "Annabi Muhammad (SAW) shi ne mafificin manzon a cikin Annabawan bature 92 Page 93 Page Allah kuma shi ne mafi daraja. Saba masa sabawa Allah ne, a cikin saba masa kuma akwai masu yi masa kage, duk wadda ya yiwa Annabi kagi ya kafirta, duk wadda ya bautawa wani ba Allah baya kafirta, Ka so annabi mafi kololuwar soyayya ka bi dukkanin umarninsa a cikin umarninsa ba za ka ci karo da shirya ko wani abu da zai sabawa al'kur'ani saboda haka karya suke shi yasa nake sanar da ku ku yi karatu, a cikin ilimi ne kadai za ku karkade wannan datti, domin abubuwa suna da yawa wadanda suka nuna karya ce karara ake yi masa wannan ya ta faruwa bayan wafatinsa, za mu samu lokaci da daliban ilimi masu zuwa garuruwa don wa'azantarwa da da'awa domin su fara yaki da irin wadannan muggun 'yan ta'adda acikin addinin musulunci Insha" ya dan yi shiru yana duban jama'a daga bisani ya ce "Za ku iya tafiya sai bayan magriba za mu dora”. Bayan kowa ya watse a masallacin jikin gidan Shehul Islam, Shehul Islam ya ce "Ranka ya dade kai ne da kanka cikin wannan badda kama?" Sarki Muhammad yayi shiru yana kallon Shehul Islam har Shehul Islam yayi tsammanin akwai abin da Sarki yake nazari akansa har yayi shirin yi masa Magana sai Sarki Muhammad ya ce "Ya kai Shehul Islam, na zo gare ka ne domin ka gaya min gaskiya, ka kuma gaya min laifukana da Hakimi Nur ne kadai ke iya tunkara ta ya sanar da ni, a fadin duniya, na san ina da matsaloli da suke yawo a cikin hakimai na, suna tattaunawa a junansu, talakawana suna tattaunawa a junansu Sarakai suna tattaunawa a junansu, amma matsalar da nake da ita ana tsoron tunkara ta da ita,wacce koma baya nakai birnin Bahara, wane ci gaba na kai Birnin Bahara?" Koda Shehul Islam ya ji wannan batu sai ya dago da kai ya dubi Sarki ya ce "Ranka ya dade, na ganka cikin shiga ta badda kama, ko zan iya mikewa mu tashi mu shiga gari mu zagaya majalisu na talakawa, mu shiga kasuwa mu ji kukensu?" bature 94 Page Sarki Muhammad ya ce "Ba ni da karfin jiki domin yanayin jikina amma zan jure ka shirya mu je?" Ba tare da bata lokaci ba Shehul Islam ya mike gami da zuwa cikin gida yayi shiri yadda ba kowa zai gane shi ba, ya fito ya samu sarki suka kama hanya a dawakai
🏠