NOVEL SHARES -

TSUTSAR NAMA BOOK 1 One

Page 32 of 42

. Ta yi shiru tana wani tunani “Naji Mama ta ce ciwonka Sihiri ne ba cuta ce daga Allah ba kirkirarta aka yi”. "Me kika ce?" Ta kalle shi "Na ji suna hira da Hindu, ta ce tana yi maka magani a boye batare da sanin kowa ba, tana addu'a tana tofa maka duk ranar da ta kasance kana tare da ita, a turakarka". Maganar ta dake zuciyarsa sai da har ya samu wani lokaci sannan ya dawo hayyacinsa ya dubi Zahra ya ce "Na gaji da zama ki rike hannayena mu koma ciki, ga magriba nan ta karato”. Lokacin da sarauniya Siyama ta koma dakinta sai ta samu kuyanganta abokiyar sirrinta ta kut da kut ta zauna ta rubuta sako zuwa ga Waziri na bukatar son ganinsa cikin gaggawa da bayanin a takaice abin da ya sa ta ke son haduwar ta su saboda kada yayi kasala. Da fitar wannan hadimar tata kuwa sai ga wata yar sako daga shugaban masu aikin gidan zuwa gare ta. Ta shigo falon ta fadi ta yi gaisuwar ban girma gami da cewa "Yarima Yazid ya dawo, yana kwance a dakinsa". bȧture 89 Page Ta zaro ido cikin tsoro da fargaba "Me ya same shi me ya faru da shi? Bata jira jin ba'asi ba ta riga wannan yar sakon fita daga dakin ta fice zuwa sashin 'ya'yan Sarki maza ta wata karamar kofa wacce ita take sadaka da bangarensu, kuma bisa al'ada babu wadda yake shiga ta kofar sai Yarima shi ma sai yayi izini an kuma amshi izinin nasa am bashi dama, iyayensu da 'yan uwansa mata na iya kai musu ziyara duk lokacin da suka so, ta isa falonsa a lokacin yana kishingide a kan gadonsa na alfarmababu riga a jikinsa ga hannunsa an daure masa da wani farin kyalle" da sauri ta kara sa "Dana Yarima, me ya faru da kai?" Ta kama hannun tana kallo "Ba wani abu bane yanka ne kar ki damu?" "Me ya faru kagaya min wasu ne suka tare ku?" "Shugaban dakarun Benjamin.. amma kar ki damu na bishi na dasa masa ciwon da ya fi karfin wadda ya dasa min akwai katon yanka a cikinsa?" Tana kallonsa tana saurarensa cikin rashin fahimta "She Benjamin ya iya yi maka wannan raunin a wane dalili kar ka bata komai dana Sarki yana tura ku ne domin ku je ku gwada fasaharku ta iya siyasa da da yadda za ku iya kwantar da kai ku samu nasara wajen makiyanku, idan ya tura ku yaki, yana so ku je ku nuna tsantsar jarumta ta damatsa, da karfintakobi, ammaa duk sanda ya tura ku sulhu sulhun nan kadai yake bukata, ba yaki, me ka je ka aikata ya kai dana". Ya girgiza kai yana ciccije baki “Mama nasani, ki kwantar da hankalinki, ba yaki nay i ba, Benjamin yayi haka ne domin ya turo sako zuwa ga Sarki, don ganin sun shirya yaki Mama, sun daina shakkar masarautarmu, saboda baba ya gaza tabuka komai, lokaci yayi da Baba zai dauki kujerar mulkinsa ya dankamin domin kada martabar kasarmu da Kalmar Allah ta yi kasa a wannan nahiyar bature 90 Page kasashen da suke tsoron koda inuwarmu yanzu suna iya fito na fito da mu kaico" "Ka tafka kuskure Yazid ka tafka kuskure wannan nakasu ne wannan nakusu ne,me ya faru". Duk abin da ya faru ya sanar da ita ta kama girgiza kai "Kayi kuskure, wannan labarin ba zai je kunnen Sarki ba, dole a rufe baki a kan maganar fadanka da Benjamin za mu basu labarin saranka da yayi ne kadai a kafada". "Ba ni da ko shakka ban yi wani abu a bisa kuskure ba, nay i abu ne domin nuna karfin ran jinin musulmi Benjamin yana daukar cewa shi zarra ne, na kuma ladaftar da shi na nuna masa ruwa ba sa'an Kwando bane, ki kwantar da hankalinki babu wani abu da zai sauya". Ta ci gaba da girgiza kai “Baka san komai a kai ba Yazid, baka san mene ne burin da manufar mahaifinka ba, tura ka gwaji da yayi kai da dan uwanka yana son ya auna tunaninku da kuma hikimarku ne, idan Abbas yayi nasara ba z aka taba zamowa Sarki ba, domin Sarki zai bada sunan Yazid". Yayi shiru yana kallonta "Mene ne idan Abbas ya zama Sarki ni ban zama ba, me kike shakka da shayi, Abbas kani na ne, ina alfahari da shi, idan har fi ni cancanta zamowa Sarki zan goya masa baya kamar yadda shi ma na san idan na fishi cancanta zai goya min baya". "Baka da wayu baka san abin da kake yi ba Yazid, idan har Abbas ya zama Sarki zai tarwatsa komai namu, zai salwantar da ruhin duk wani dana a doron kasa?" "A wacce hujjar, da dalili, waye ya gaya miki wannan Mama ki guje maganganun irin wadannan domin rayuwarki zata zama gajera, 'ya'ya Sarki Muhammad ne jikokin Farsi masu Sarauta daular musulunci, tarbiya da kaunar juna a jinin jikinmu, take, matukar bature 91 | Page bamu zalunci dan uwanmu ko nuna masa rashin goyan baya, ko fitowa mu yake shi ba na tabbata zai ba mu kariya zai kuma daga darajarmu". Ya koma ya kwanta tayi suroro tana dubansa wannan lamari shi ke tayar mata da hankali bata da wata mafita illa ta fice daga dakin zuwa ga jin ba'asi dangane da sakonta data aika. Lokacin da Sarki Muhammad ya isa fadarsa sai ya yi wata irin shiga ta irin attajirai ba sarakai ba, ba tare da kowa ya sani ba ya fice ta kofar da ya saba fita in zai yi irin wannan fitar ta basaja. Kai tsaye gidan Imam Muslim ya isa, tunda ya lura mutane na fitowa daga dakin
🏠